Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025
Published: November 30, 2025 at 7:44 AM | By: Bala Hassan | Updated: November 30, 2025

JIHAR NASARAWA TA ƊAUKI KYAUTAR KWALLON KAFAR KURAME.

Ƙungiyar Kwallon Kafa na Kurame Deaf, ta jihar Nasarawa a Tarayyar Najeriya ta lashe kofin gasar a bana.

Gasar wadda ta ƙunshi jihohi goma, ciki har da Nasarawa, Rivers, Niger, Kaduna, Kano, Kebbi, da masu masaukin baki, Plateau, Adamawa, Bauchi, da FCT, Abuja, ta fara ne a ranar 19 ga Nuwamba, 2025, a cibiyoyi daban-daban a Jos, Jihar Plateau.

Sakatariyar Wasanni ta Musamman na Jihar Nasarawa, Ms Patricia David Oshuwayine, ita ta wakilci Ma’aikatar Matasa da Ci gaban Wasanni ta Jihar Nasarawa a gasar.

Kwamishinan Ci gaban Matasa da Wasanni na Jihar Nasarawa, Hon. Kwanta Yakubu, ya taya Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Kurame na Jihar murna nasarar da suka samu a gasar cin kofin ƙwallon ƙafa ta ƙasa ta karo na 6 da aka gudanar a Jos, Jihar Plateau.

Kwanta ya ce, “Makonni kaɗan da suka gabata, na haɗu da membobin ƙungiyar a sansaninsu da ke Lafia, kafin fara gasar, kuma na ƙarfafa musu gwiwa don su yi duk mai yiwuwa don faranta wa Gwamna Abdullahi Sule da Jihar rai ta hanyar lashe gasar a Jos, kuma zan gabatar da su ga Gwamna.

“A yau, Gwamna Abdullahi Sule da dukkan al’umar Jihar suna alfahari da rawar da ƙungiyar ta taka.

“‘Yan wasanmu masu hazaka sun fafata da manyan ƙungiyoyi daga ko’ina cikin ƙasar, kuma daga ƙarshe sun yi nasara

“Muna yi wa sabbin zakarun ƙasa alƙawarin tarba mai kyau da kuma shirya ya musu liyafa ta musamman a Lafia, Babban Birnin Jiha,” in ji Kwamishinan.

Tawagar ƙungiyar Nasarawa ta samu wannan nasararne bayan da ta doke tawagar ƙungiyar kwallon kafa ta Kurame na Jihar Kaduna da ci 1-0 a ranar Asabar 29 ga watan Nuwamban 2025.

Da yake zantawa da yan jarida mai horas da ƙungiyar na jihar Nasarawa Jafar Umar yace kafin lashe wannan gasar ta wagar Nasarawa ta doke masu ma saukin baki jihar Plateau,Adamawa,Kebbi,da jihar Niger.

Kamar yadda Jami’in hulda da jama’a na Ma’aikatar Matasa da Ci gaban Wasanni na Jihar Nasarawa, Eche Amos ya fitar a wata ta karda da ya rabawa mane ma labarai.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba!
Next Post: Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce!

Karin Labarai Masu Alaka

CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya Wasanni
Arsenal Ta Doke Manchester City 3-0, Ta Ɗauki Kofin Community Shield Wasanni
Sarkin Gombe Ya Ziyarci Gwamna Inuwa Yahaya Afrika
Salmanu: Ci Gaban Wikki Tourist FC Shine A Gaba Na Wasanni
Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
CAF, Zata Ci Tarar Wasu Kasashe AFCON 2025 Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke Amurka
  • Suvr Jahun: Ya Kamata Obasanjo Ya Bar Al’umar Ƙasa Su Fito Da Wadda Suke So 2027 Najeriya
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai
  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
  • Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
  • Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan Labarai
  • Ruwa Kamar Da Bakin Kwarya Ya Haifar Da Mutuwar Mutane A Nairobi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.