Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Majalisar Dokokin Filato Ta Kare Kudirin Alawus Ga Tsofaffin ‘Yan Majalisa
Published: July 21, 2026 at 12:37 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Majalisar Dokokin jihar Filato ta yi karin haske kan kudirin dokar da ke neman samar da tsarin alawus na wata-wata ga tsofaffin ‘yan majalisar jihar, bayan ce-ce-ku-cen da kudirin ya haifar a tsakanin al’umma.

A makon da ya gabata ne majalisar ta gabatar da kudirin dokar, wanda ya tsallake karatu na farko da na biyu a rana guda. Kudirin na neman bai wa tsofaffin shugabannin majalisa da mambobin da suka kammala wa’adinsu damar samun alawus na wata-wata mai kama da pansho.

Shugaban Kwamitin Kudi na Majalisar Dokokin Jihar Filato, kuma mamba mai wakiltar Rukuba/Irigwe, Eli Bako Ankala, wanda ya gabatar da kudirin, ya ce manufarsa ita ce ‘yan majalisar da ke kan mulki su ware wani kaso daga alawus dinsu domin tallafa wa tsofaffin ‘yan majalisar.

Ya bayyana cewa kudaden ba za su fito daga gwamnatin zartarwa ba, sai dai daga gudunmawar da ‘yan majalisar za su rika bayarwa daga alawus dinsu.

Sai dai kungiyoyin farar hula da na kwadago a jihar sun yi watsi da kudirin, suna zargin cewa ba a bayyana cikakkun bayanansa ga jama’a ba.

Shugaban Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) reshen Jihar Filato, Kwamared Eugene Manji, ya ce sun bai wa majalisar wa’adin zuwa ranar 30 ga watan Yuli ta janye kudirin, yana mai gargadin cewa idan ba a yi hakan ba, za su dauki matakin kulle harabar majalisar.

A halin yanzu dai ana ci gaba da sa ido kan yadda rikicin ra’ayi tsakanin majalisar da kungiyoyin farar hula da na kwadago zai kaya idan wa’adin ya cika.

Daga Jos, Zainab Babaji ta aiko mana da rahoto

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/07/AUD-20260721-WA0024.mp3
Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Jaddada Buƙatar Kare Rayukan ‘Yan Afirka A Taron ECOWAS
Next Post: Kungiyar Miyetti Allah Ta Bukaci Mambobinta Su Marawa Dr. Jamilu Isiyaku Gwamna Baya A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar IMF Tana Naziri Domin Kara Bada Lamuni Ga Kasar Zambiya Afrika
Amurka Zata Tantance Fararen Fata ‘Yan Afirka Ta Kudu Afrika
Sojoji Sunkai Farmaki Gidan Dan Adawa A Kasar Uganda Bobi Wine Afrika
Angano Gawar Wani Dan Myanmar A Arewacin New York Afrika
Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
Hukumar Kare Hakkin ‘Yan Jarida Tace Isra’ila Ce Ta Kashe ‘Yan Jarida Kashi Biyu Bisa Uku Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Spain Ta Rufe Sararin Saman Kasar Amurka
  • ‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke Wasanni
  • Sanata Goje Yayi Watsi Da Fidda ‘Yan Takarar APC A Gombe Afrika
  • Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu Afrika
  • Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11 Najeriya
  • CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Kama Wani Da Abubuwan Fashewa A Zamfara Najeriya
  • Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.