Majalisar Dokokin jihar Filato ta yi karin haske kan kudirin dokar da ke neman samar da tsarin alawus na wata-wata ga tsofaffin ‘yan majalisar jihar, bayan ce-ce-ku-cen da kudirin ya haifar a tsakanin al’umma.
A makon da ya gabata ne majalisar ta gabatar da kudirin dokar, wanda ya tsallake karatu na farko da na biyu a rana guda. Kudirin na neman bai wa tsofaffin shugabannin majalisa da mambobin da suka kammala wa’adinsu damar samun alawus na wata-wata mai kama da pansho.
Shugaban Kwamitin Kudi na Majalisar Dokokin Jihar Filato, kuma mamba mai wakiltar Rukuba/Irigwe, Eli Bako Ankala, wanda ya gabatar da kudirin, ya ce manufarsa ita ce ‘yan majalisar da ke kan mulki su ware wani kaso daga alawus dinsu domin tallafa wa tsofaffin ‘yan majalisar.
Ya bayyana cewa kudaden ba za su fito daga gwamnatin zartarwa ba, sai dai daga gudunmawar da ‘yan majalisar za su rika bayarwa daga alawus dinsu.
Sai dai kungiyoyin farar hula da na kwadago a jihar sun yi watsi da kudirin, suna zargin cewa ba a bayyana cikakkun bayanansa ga jama’a ba.
Shugaban Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) reshen Jihar Filato, Kwamared Eugene Manji, ya ce sun bai wa majalisar wa’adin zuwa ranar 30 ga watan Yuli ta janye kudirin, yana mai gargadin cewa idan ba a yi hakan ba, za su dauki matakin kulle harabar majalisar.
A halin yanzu dai ana ci gaba da sa ido kan yadda rikicin ra’ayi tsakanin majalisar da kungiyoyin farar hula da na kwadago zai kaya idan wa’adin ya cika.
Daga Jos, Zainab Babaji ta aiko mana da rahoto


