Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya jagoranci taron majalisar haɗin gwiwa kan ayyukan ci gaban jihar, wanda shi ne karo na takwas, domin duba yadda ake tsara da aiwatar da ayyukan raya jihar cikin tsari da inganci.
Taron, wanda shi ne na farko tun bayan kafa ƙananan hukumomin ci gaba guda 13 (LCDAs), ya mayar da sabbin hukumomin cikin tsarin tsare-tsaren ci gaba da aiwatar da ayyukan gwamnati a jihar.
Da yake bayyana sakamakon taron, Darakta-Janar na Hukumar Haɗin Gwiwar Ayyukan Ci Gaba da Muhimman Ayyuka ta Jihar Gombe (JPDESA), Dr. Mahmood Yusuf ya ce majalisar ta amince da wasu muhimman ayyuka da ƙarin ayyukan more rayuwa domin magance buƙatun da suka taso a fannonin ci gaban jihar.
Daga cikin manyan abubuwan da majalisar ta amince da su akwai inganta da gyara Fadar Mai Martaba Sarkin Gombe, Alhaji (Dr.) Abubakar Shehu Abubakar III, CFR.
Bldr. Mahmoud Yusuf ya ce matakin na cikin ƙoƙarin gwamnatin Gwamna Inuwa Yahaya na kare da inganta muhimman cibiyoyin gargajiya, tare da samar musu da abubuwan more rayuwa da suka dace da matsayinsu.
Ya ƙara da cewa inganta fadar zai taimaka wajen ƙawata muhalli, inganta ayyukan fadar da kuma samar da yanayi mai kyau ga harkokin gudanarwa.
A cewarsa, matakin ya kuma nuna irin muhimmancin da gwamnatin jihar ke bai wa sarakunan gargajiya wajen tabbatar da zaman lafiya, haɗin kan al’umma da kuma tallafa wa manufofin gwamnati na ci gaba.
A wani mataki kuma, majalisar ta amince da samar da ƙarin muhimman abubuwan more rayuwa a sabbin ƙananan hukumomin ci gaba guda 13, domin tabbatar da cewa sun fara aiki cikin sauƙi da inganci.
Darakta-Janar ɗin ya bayyana cewa duk da cewa an kammala samar da gine-ginen sabbin ƙananan hukumomin, gwamnati ta ga ya dace a ƙara wasu muhimman kayan aiki da ayyuka domin ba su damar fara gudanar da ayyukansu ba tare da tsaiko ba.
Daga cikin abubuwan da aka amince da samarwa akwai na’urorin samar da wutar lantarki ta hasken rana, rijiyoyin burtsatse masu amfani da hasken rana da kuma na’urorin sa ido na tsaro, baya ga sauran muhimman kayan more rayuwa.
Ya ce samar da wutar lantarki ta hasken rana zai taimaka wajen tabbatar da samun ingantaccen wutar lantarki a sabbin cibiyoyin, yayin da rijiyoyin burtsatse masu amfani da hasken rana za su samar da ruwa mai ɗorewa ga ma’aikata da sauran masu amfani da cibiyoyin.
Ya ƙara da cewa na’urorin sa ido na tsaro za su taimaka wajen ƙarfafa tsaro, kare kadarorin gwamnati da kuma samar da ingantaccen yanayi ga ma’aikata da al’ummar da za su riƙa amfani da ayyukan sabbin ƙananan hukumomin.
Majalisar ta kuma yi nazari kan ayyukan raya jihar da ake ci gaba da gudanarwa, tare da duba wasu ƙarin matakan da ake buƙata domin tabbatar da ci gaba da samun nasarar ayyukan raya jihar.


