Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Pads To Prosperity: NEDC Ta Horar Da Mata 280 Kan Kera Pads A Gombe
Published: August 14, 2026 at 8:02 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar Raya Arewa maso Gabashin Najeriya (NEDC) ta yi alkawarin ci gaba da sanya ido da kuma tallafa wa mata 280 da suka samu horo a karkashin shirin “Pads to Prosperity Community Pad-Making Enterprise Programme” a Jihar Gombe.

Mai Kula da ayyukan NEDC a Jihar Gombe, Architect Usman Muhammad, ne ya bayyana hakan a wajen bikin rufe shirin horaswar da aka gudanar a Gombe.

Ya ce hukumar ta himmatu wajen inganta rayuwar al’ummar yankin Arewa maso Gabas ta hanyar samar da shirye-shiryen da za su bunkasa kwarewa, samar da ayyukan yi da kuma dogaro da kai.

Architect Usman ya yaba wa mahalarta shirin bisa jajircewa da hadin kan da suka nuna a lokacin horaswar, inda ya bayyana cewa an zabo mahalarta daga kananan hukumomin Dukku, Funakaye, Gombe da Yamaltu Deba a matsayin wuraren gwajin shirin.

Ya bukaci wadanda suka amfana da horon da su yi amfani da ilimin da suka samu wajen kafa kananan sana’o’i da za su taimaka wajen inganta rayuwarsu da ta al’ummominsu.

Shi ma da yake magana, Rufai Lawan Baba Manu, ya ce za a rika bibiyar shirin na tsawon watanni shida tare da hadin gwiwar wasu kungiyoyi, domin tabbatar da cewa mahalarta sun samu damar mayar da kwarewar da suka koya zuwa sana’o’i masu dorewa.

Ya ce shirin na da manufar gina lafiya, samar da arziki da sauya rayuwar al’umma, musamman ta hanyar bai wa mata damar samun sana’a da dogaro da kai.

Rufai Baba Manu ya kuma yaba wa mahalarta bisa kyakkyawan hali, jajircewa da ladabtarwa da suka nuna, tare da tabbatar musu da cewa NEDC za ta ci gaba da ba su goyon baya da hadin kai.

A sakonnin fatan alheri, Hajiya Fatima Umar Abubakar daga Ma’aikatar Harkokin Mata ta jihar Gombe, Dr. Gazali Abdulhamid, Shugaban kwalejin Ilimi ta Tarayya a Gombe, Malam Ibrahim Yusuf na kungiyoyin farar hula, da Hajiya Maimuna Abubakar ta Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Kasa (NOA), Gombe, da sauran masu ruwa da tsaki, sun yaba wa NEDC kan kokarin da take yi wajen sauya rayuwar al’umma ta hanyar samar da sana’o’i da dabarun dogaro da kai.

Sun ce irin wadannan shirye-shirye na taimakawa wajen rage radadin matsin tattalin arziki da samar da hanyoyin samun kudin shiga ga iyalai.

Sun kuma bukaci wadanda suka kammala horon da su zama masu horas da wasu (Training of Trainers), domin su yada ilimin da suka samu ga matasa da sauran al’umma, musamman a yankunansu.

Shirin Pads to Prosperity wanda NEDC ta dauki nauyin gudanarwa, tare da hadin gwiwar Virtuous Reusable Pads, ya mayar da hankali kan inganta lafiyar mata, samar da arziki da kuma sauya al’umma ta hanyar koyar da sana’ar kera kayan tsaftar mata da bunkasa kananan sana’o’i.

Afrika, Kimiya, Kiwon Lafiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sana'o'i, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: CP Chuso Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Gwiwar Hukumomin Tsaro A Gombe
Next Post: NDPHC Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Gombe Wajen Inganta Wutar Lantarki

Karin Labarai Masu Alaka

Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Zata Tabbatar Da Tsagaita Wuta A Kwango Afrika
Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan Labarai
Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000 Najeriya
Iran Tace Farisa Zata Kai Hari Kan Mayakan Amurka Amurka
Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak Labarai
An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Faransa Ta Karyata Cire Afirka Ta Kudu Daga G7 Afrika
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Afrika
  • Fadar Sarkin Musulmi: Talata Ne 1 Ga Watan Sha’aban Na 1447AH Najeriya
  • Kungiyar EU Zata Taimakawa Somalia Da Kudade Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Gaddafi A Gidansa Dake Kasar Libya Afrika
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wasu Yara 50 Sun Kubuta Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.