Gwamnan Jihar Gombe kuma Visitor na Jami’ar jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya amince da ƙarin Naira miliyan 148.762 a matsayin tallafin wata-wata ga Jami’ar Jihar Gombe, domin sauƙaƙa cikakken aiwatar da sabon tsarin albashi da aka fi sani da Consolidated Academic Tool Allowance (CATA).
Ƙarin tallafin zai fara aiki ne daga Oktoba 2026, kamar yadda Sakataren Gwamnatin jihar Gombe, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, ya bayyana yayin isar da amincewar gwamnan.
Farfesa Njodi ya ce matakin wani ɓangare ne na ƙudurin Gwamna Inuwa Yahaya na magance matsalolin da suka taso sakamakon yarjejeniyar Gwamnatin Tarayya da ASUU ta shekarar 2025.
A cewarsa, ƙarin tallafin da ya kai kashi 56 cikin 100, zai ƙarfafa ikon jami’ar wajen biyan haƙƙoƙin ma’aikatanta tare da samar da isasshen tanadi a kasafin kuɗin jami’ar domin aiwatar da sabon tsarin albashin a cikin Kasafin Ƙarin Kuɗi na 2026.
Ana sa ran Majalisar Dokokin Jihar Gombe za ta duba kasafin ƙarin kuɗin a watan Satumba 2026.
Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma umarci shugabancin jami’ar da ya fara dukkan matakan da suka dace domin biyan bashin CATA da aka tara.
Baya ga aiwatar da CATA, gwamnan ya umarci jami’ar da ta samar da hanyoyin cikin gida domin biyan sauran basussukan ma’aikata a hankali, ciki har da bashin ƙarin albashin kashi 25 da kashi 35 cikin 100, mafi ƙarancin albashi, da Earned Academic Allowances.
Gwamnatin ta ce za a biya waɗannan basussuka ne a matakai, tare da la’akari da ɗorewar kuɗaɗen jami’ar da kuma buƙatar ci gaba da gudanar da karatu ba tare da tsaiko ba.
A wani mataki na magance ƙalubalen kuɗaɗen ilimi, Majalisar Dokokin Jihar Gombe ta amince da dokar kafa Asusun Amintaccen Ilimi na Jihar Gombe, wanda ake sa ran fara aiki a watan Oktoba 2026.
An tsara asusun ne domin samar da ingantaccen tsarin samun kuɗaɗen ilimi, musamman ga Jami’ar Jihar Gombe da sauran manyan makarantun gwamnati mallakin jihar.
Gwamnatin ta ce asusun zai ƙara mata damar biyan buƙatun yau da kullum da na raya manyan makarantun jihar, tare da samar da ingantacciyar hanyar kula da jin daɗin ma’aikata da sauran buƙatun jami’o’i.
Gwamnatin jihar Gombe ta kuma yi kira ga Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) da ta yi la’akari da matakan da aka riga aka ɗauka da kuma tabbacin da gwamnati ta bayar na magance matsalolin da suka shafi ƙungiyoyin ma’aikatan ilimi da waɗanda ba na ilimi ba.

Gwamnatin Inuwa Yahaya ta sake jaddada aniyarta ta yin aiki tare da ASUU, shugabancin jami’ar da sauran masu ruwa da tsaki, domin tabbatar da zaman lafiya a masana’antar ilimi, daidaiton harkokin karatu da ci gaba da bunƙasar Jami’ar Jihar Gombe.


