Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta yi kira ga jam’iyyun siyasa, ’yan takara da magoya bayansu da su guji tashin hankali, daba, kalaman ƙiyayya da duk wani nau’in rashin da’a a harkokin zaɓe, gabanin zaɓen cike gurbin kujerar Majalisar Wakilai na ranar 19 ga Satumba da kuma Babban Zaɓen 2027.
Kwamishinan ’Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, mnips, fwc, psc(+), ya yi wannan kiran ne a lokacin wani taron haɗin gwiwa na tsaro da sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin hukumomin tsaro da jam’iyyun siyasa a jihar.
Kwamishinan ya ce taron wata dama ce ta sake jaddada aniyar dukkan masu ruwa da tsaki wajen tabbatar da gudanar da zaɓuka cikin lumana, gaskiya da adalci a Jihar Gombe.
Ya ce duk da cewa fafatawar siyasa muhimmin ɓangare ne na dimokuraɗiyya, dole ne a gudanar da ita cikin bin doka, mutunta juna da kuma ɗabi’ar siyasa mai nagarta.
CP Chuso ya kuma nuna damuwa kan yadda ake ƙara amfani da kafafen sada zumunta wajen aikata abin da ya kira “dijital daba”, ta hanyar yin barazana ga abokan hamayya, yaɗa saƙonnin tayar da hankali, ƙirƙira da yaɗa labaran ƙarya da kuma tunzura jama’a.
Ya buƙaci ’yan siyasa da magoya bayansu da su yi taka-tsantsan wajen amfani da kafafen sada zumunta, tare da tabbatar da sahihancin bayanan da suke yaɗawa kafin su rarraba su.
Kwamishinan ya kuma buƙaci jam’iyyun siyasa da ’yan takara su wayar da kan magoya bayansu, musamman matasa, tare da hana amfani da su wajen aikata tashin hankali.
Ya ce babu wata manufa ta siyasa da ta kai darajar rayuwar mutum, ’yancinsa ko makomarsa.
CP Chuso ya tabbatar da cewa hukumomin tsaro a Jihar Gombe za su ci gaba da samar da ingantaccen yanayi da zai ba jama’a damar gudanar da ayyukansu na dimokuraɗiyya cikin kwanciyar hankali.
Ya ce rundunar za ta kasance mai ƙwarewa, rashin son kai da kuma tsayin daka wajen tabbatar da bin doka, tare da ɗaukar matakin da ya dace kan duk wanda ya yi ƙoƙarin kawo cikas ga zaman lafiyar jihar.
Kwamishinan ya kuma shawarci ’yan siyasa da su yi amfani da hanyoyin doka da kundin tsarin mulki wajen warware duk wata takaddama da za ta taso, maimakon komawa ga tashin hankali ko ɗaukar doka a hannu.
A nasu ɓangaren, wakilan jam’iyyun siyasa da suka haɗa da APC, PDP, ADC da Labour Party, da Sani Abubakar Dadawagga Shugaban na Jam’iyar SDP sauran jam’iyyu, sun yaba wa Kwamishinan ’Yan Sandan bisa shirya taron.
Sun ce irin wannan mataki zai taimaka wajen tabbatar da yanayin siyasa mai cike da zaman lafiya a jihar, tare da ba da tabbacin cewa za su gudanar da harkokinsu bisa doka da ƙa’idojin da hukumomin zaɓe suka gindaya.
Wakilan jam’iyyun sun kuma tabbatar da aniyarsu ta bin doka da oda, tare da gudanar da yakin neman zaɓe da sauran harkokin siyasa cikin lumana.
Shi ma wakilin Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC, a Jihar Gombe, Alhaji Aliko Muhammad, ya tabbatar da shirye-shiryen hukumar na gudanar da zaɓuka cikin ’yanci, adalci da sahihanci.
Ya yi kira ga jam’iyyun siyasa da ’yan takara da su kiyaye doka da oda, tare da bin ƙa’idojin da hukumar ta tanada a duk tsawon lokacin gudanar da harkokin zaɓe.
Masu ruwa da tsaki sun bayyana yarjejeniyar zaman lafiyar a matsayin wani muhimmin mataki na tabbatar da cewa zaɓen cike gurbin ranar 19 ga Satumba da kuma Babban Zaɓen 2027 sun gudana cikin kwanciyar hankali.
Sun kuma jaddada cewa kare zaman lafiyar Jihar Gombe nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa, inda suka yi alƙawarin fafatawa ba tare da tashin hankali ba, sabani ba tare da ƙiyayya ba, tare da amfani da fasahar zamani wajen wayar da kan jama’a maimakon tunzura su.


