Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • NUJ Ta Kai Ziyarar Jaje GMC Bayan Gobara Ta Lalata Ginin Sashen Talabijin Afrika
  • ANNOUR Ta Raba Kayan Makaranta Na CFA Miliyan 5.5 Ga Yara A Douala Afrika
  • Sabbin Shugabannin NUJ Bauchi Sun Sha Alwashin Inganta Aikin Jarida Afrika
  • INEC Ta Ce Zaɓen Gombe, Kwami Da Funakaye Yana Gudana Cikin Lumana Afrika
  • GOSERC Ta NemI Haɗin Kan Masu Ruwa Da Tsaki Wajen Inganta Wutar Lantarki A Gombe Afrika

Ƙungiyoyin Fararen Hula Sun Ƙarfafa Yaƙi Da Gurɓacewar Muhalli A Kaduna
Published: September 20, 2026 at 7:58 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: September 20, 2026

A wani ɓangare na ayyukan bikin Ranar Tsaftace Muhalli ta Duniya ta 2026 kungiyoyin fararen hula, shugabannin al’umma da masu sa-kai sun haɗa ƙarfi wajen gudanar da aikin tsaftace muhalli a wasu sassan birnin Kadunan Najeriya tare da wayar da kan jama’a kan muhimmancin kare muhalli.

An gudanar da bikin Ranar Tsaftace Muhalli ta Duniya ta 2026 ne ƙarƙashin taken “Daga Faranti Masu Tsabta zuwa Birane Masu Tsabta”, wanda ke jaddada buƙatar rage ɓarnar abinci da kuma inganta tsafta domin samar da al’ummomi masu lafiya da ɗorewar muhalli.

Da take magana yayin aikin tsaftace muhalli a Kaduna, Habiba Suleman, wadda ta shirya ayyukan Ranar Tsaftace Muhalli ta Duniya na 2026 a Kaduna kuma shugabar Plogging Nigeria, Jami’ar Jihar Kaduna (KASU), ta ce ƙungiyoyi da dama sun shiga aikin da nufin tsaftace wasu sassan Kaduna tare da ƙarfafa wa mazauna garin gwiwa su ƙara ɗaukar nauyin kula da muhallinsu.

Ta ce halartar ƙungiyoyin fararen hula, shugabannin al’umma da masu sa-kai na nuna muhimmancin haɗin gwiwa wajen magance matsalar gurɓacewar muhalli da kuma sauran ƙalubalen muhalli da ke addabar al’umma.

A cewarta, aikin ba wai tattara shara kaɗai ake nufi da shi ba, har ma da wayar da kan jama’a game da yadda ya kamata a zubar da shara, muhimmancin sake amfani da kayan da za a iya sarrafawa, da kuma buƙatar kiyaye tsaftar wuraren jama’a.

Shi ma da yake magana, Shugaban Sashen Sadarwa da Dabarun Aiki na African Climate Reporters (ACR), Ibrahima Yakubu, ya ce ACR ta shiga aikin tsaftace muhalli ne a matsayin wani ɓangare na ƙudurin ƙungiyar na kare muhalli da kuma yaƙi da sauyin yanayi.

Ya ce kafafen yaɗa labarai na da muhimmiyar rawa wajen ilmantar da jama’a kan yadda ake sarrafa shara, gurɓacewar muhalli da kuma ƙalubalen muhalli da ke da alaƙa da sauyin yanayi.

Ibrahima Yakubu ya jaddada cewa tabbatar da tsaftar Kaduna na buƙatar haɗin kan hukumomin gwamnati, ƙungiyoyin fararen hula, shugabannin al’umma, ‘yan kasuwa, kafafen yaɗa labarai da kuma mazauna birnin.

Ya ƙara da cewa African Climate Reporters za ta ci gaba da inganta aikin jaridun da suka shafi sauyin yanayi da muhalli, a matsayin wata hanya ta wayar da kan jama’a, ƙarfafa sauyin ɗabi’a da kuma tattara al’umma domin ɗaukar matakan dakile lalacewar muhalli.

Kimiya, Labarai

Post navigation

Previous Post: Sabbin Shugabannin NUJ Bauchi Sun Sha Alwashin Inganta Aikin Jarida
Next Post: ANNOUR Ta Raba Kayan Makaranta Na CFA Miliyan 5.5 Ga Yara A Douala

Karin Labarai Masu Alaka

Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar Afrika
Shugaba Yoweri Musevini Ya Zamo Shugaban Uganda Na 7 Yana Da Shekaru 81 Kuma Ya Shafe Shekaru 50 A Mulki Labarai
Gwamna Ahmad Aliyu Na Jihar Sokoto Ya Gabatar Da Kasafin Fiye Da Naira Biliyan 700 Labarai
Shugaban Trump: Washington Zatayi Cinikayya Da Indiya Amurka
Isra’ila Takai Hare Hare Birnin Tehran Afrika
Pasto Yohanna Buru Ya Jagoranci Kiristoci Wajen Bikin Mauludi Tare Da Musulmi A Kaduna Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • NUJ Ta Kai Ziyarar Jaje GMC Bayan Gobara Ta Lalata Ginin Sashen Talabijin
  • ANNOUR Ta Raba Kayan Makaranta Na CFA Miliyan 5.5 Ga Yara A Douala
  • Ƙungiyoyin Fararen Hula Sun Ƙarfafa Yaƙi Da Gurɓacewar Muhalli A Kaduna
  • Sabbin Shugabannin NUJ Bauchi Sun Sha Alwashin Inganta Aikin Jarida
  • INEC Ta Ce Zaɓen Gombe, Kwami Da Funakaye Yana Gudana Cikin Lumana

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Tabada Tabbacin Cigaba Da Rufe Mashigar Hormuz Afrika
  • ACReSAL Ta Tallafa Wa FMC Kumo, Ta Shuka Bishiyoyi Tare Da Gyara Magudanan Ruwa Afrika
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Zata Tabbatar Da Tsagaita Wuta A Kwango Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika
  • Rasha: Zamu Ba Gwamnatin Venezuel Gudunmawa Sauran Duniya
  • UEFA Tana Shirin Janye Barazanar Kauracewa Gasar FIFA Wasanni
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran Afrika
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Gyara Dokar Kasafin Kudi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.