Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

RSF Ta Kasar Sudan, Tana Yin Garkuwa Da Mazauna A Yankin Darfur
Published: December 3, 2025 at 8:21 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 3, 2025

Shaidun gani da ido, da ma’aikatan agaji da kuma kwararru sun yi zargin cewa rundunar sojojin wucin gadi ta RSF ta kasar Sudan, tana yin garkuwa da mazauna wuraren da ta kama a yankin Darfur tana neman sai ‘yan’uwansu sun biya diyya kafin ta sake su.

Shaidun suka ce wadanda suka kasa biya, ana kashe su, ko a lakkada musu mummunar duka.

Babu tabbas na yawan mutanen da rundunar ta RSF take rike da su a bayan da ta kama al-Fasher, babban birnin Darfur ta Arewa a karshen watan Oktoba, amma an ce ana tsare da su a wurare dabam-dabam a sansanoni da kauyuka da dama dake yanki mai fadin kilomita 80 daga birnin, yayin da wasu ma an maida su cikin al-Fasher ana neman dubban daloli daga hannun ‘yan’uwansu.

Wadanda suka tsira da yawa da suka yi hira da Reuters sun ce ana tilasta ma ‘yan’uwanssu biyan abinda ya kama daga Fam miliyan 5 zuwa fam miliyan 60 na kudin kasar Sudan, kimanin Naira miliyan biyu zuwa miliyan 25 a kudin Najeriya, kafin a sake su, wanda kudi ne mai tsananin yawa a wannan kasa mai fama da talauci.

Wasu shaidu su 11 sun ce wadanda suka kasa biya, ana tattara su a bindige, ko a yi musu mummunar duka. Wani da ya iya samu ya biya ya kubutar da kansa, Mohammed Isma’ila, ya ce ana ba mutum kwana uku ko hudu, idan har ba a aika musu da kudin ba, sai su kashe mutum.

Yace shi da wani dan’uwansa sun tsere daga al_Fasher, amma dakarun RSF suka kama su a wani kauye kuma kowannensu sai da ya biya fam miliyan 10 na kudin Sudan, kimanin Naira miliyan hurhudu, kafin aka sake su.

Da aka nemi jin ta bakinsa, mai ba rundunar RSF shawara kan harkokin shari’a, Mohammed Mukhtar yace, wata kungiya mai adawa da tasu ce da take shigar burtu a matsayin RSF take gudanar da akasarin wannan aiki na kama mutane don neman kudin fansa a ciki da wajen birnin al-Fasher.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza
Next Post: Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Kasar Ghana Ta Rage Farashin Cocoa Afrika
Rasha Takai Hari Ukraine Da Jirgi Marar Matuki Afrika
Shugaba Bola Tinubu Ya Amince Da Inganta Wutan Lantarki A Kasar Afrika
‘Yan Bindiga A Mali Sun Kashe Direbobin Manyan Motoci Afrika
Ghana Tayi Watsi Da Yarjejeniya Akan Hakar Ma’adanai Afrika
Farashin Danyen Mai Ya Fadi A Kasuwar Duniya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Ta Tasa Keyar Wani Jirgi Shake Da Mai Sauran Duniya
  • Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka
  • Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11 Najeriya
  • Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142 Labarai
  • Gwamnatin Jihar Yobe: Ana Cin Zarafin Fursunoni A Gidan Gyaran Halin Potiskum Tsaro
  • Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka. Najeriya
  • Jagoran Kwankwasiya A Najeriya Ya Koma Jam’iyar ADC Labarai
  • Farashin Mai A Kasuwannin Duniya Yayi ƙasa Kadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.