Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka

RSF Ta Kasar Sudan, Tana Yin Garkuwa Da Mazauna A Yankin Darfur
Published: December 3, 2025 at 8:21 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 3, 2025

Shaidun gani da ido, da ma’aikatan agaji da kuma kwararru sun yi zargin cewa rundunar sojojin wucin gadi ta RSF ta kasar Sudan, tana yin garkuwa da mazauna wuraren da ta kama a yankin Darfur tana neman sai ‘yan’uwansu sun biya diyya kafin ta sake su.

Shaidun suka ce wadanda suka kasa biya, ana kashe su, ko a lakkada musu mummunar duka.

Babu tabbas na yawan mutanen da rundunar ta RSF take rike da su a bayan da ta kama al-Fasher, babban birnin Darfur ta Arewa a karshen watan Oktoba, amma an ce ana tsare da su a wurare dabam-dabam a sansanoni da kauyuka da dama dake yanki mai fadin kilomita 80 daga birnin, yayin da wasu ma an maida su cikin al-Fasher ana neman dubban daloli daga hannun ‘yan’uwansu.

Wadanda suka tsira da yawa da suka yi hira da Reuters sun ce ana tilasta ma ‘yan’uwanssu biyan abinda ya kama daga Fam miliyan 5 zuwa fam miliyan 60 na kudin kasar Sudan, kimanin Naira miliyan biyu zuwa miliyan 25 a kudin Najeriya, kafin a sake su, wanda kudi ne mai tsananin yawa a wannan kasa mai fama da talauci.

Wasu shaidu su 11 sun ce wadanda suka kasa biya, ana tattara su a bindige, ko a yi musu mummunar duka. Wani da ya iya samu ya biya ya kubutar da kansa, Mohammed Isma’ila, ya ce ana ba mutum kwana uku ko hudu, idan har ba a aika musu da kudin ba, sai su kashe mutum.

Yace shi da wani dan’uwansa sun tsere daga al_Fasher, amma dakarun RSF suka kama su a wani kauye kuma kowannensu sai da ya biya fam miliyan 10 na kudin Sudan, kimanin Naira miliyan hurhudu, kafin aka sake su.

Da aka nemi jin ta bakinsa, mai ba rundunar RSF shawara kan harkokin shari’a, Mohammed Mukhtar yace, wata kungiya mai adawa da tasu ce da take shigar burtu a matsayin RSF take gudanar da akasarin wannan aiki na kama mutane don neman kudin fansa a ciki da wajen birnin al-Fasher.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza
Next Post: Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar ISIS Ta Dauki Alhakin Harin Kasar Nijar Afrika
Amurka Ta Gabatarwa Sassan Dake Yakar Juna A Sudan da Shirin Tsagaita Wuta Afrika
Kotun Uganda Tayi Watsi Da Karar Hukumomin Kasar Afrika
Libya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashen Faransa Da Amurka Afrika
Shugabannin Kasashen Afirka Ta Tsakiya Sun Kamallah Taron Koli Afrika
Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Amurka Zata Hana Kwankwaso Shiga Kasar
  • Farfesa Inuwa Ja’afaru Yakarbi Ragamar Shugabancin Jami’ar Kashere
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga
  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
  • Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC Siyasa
  • Karo Na Biyu Cikin Kwanaki 29 An Samu Gobara A Kasuwar Katako Labarai
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031 Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
  • ‘Yan Sanda Sunce Mutum Daya Ne Yakai Hare-Haren Jami’ar Brown Da Kuma Na MIT Boston Amurka
  • Trump Da Bin Salman Da Wasu Kasashe Za Su Sa Hannu A Rikicin Sudan Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.