Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Akwai Bukatar Bincikar Umurnin Da Sakataren Tsaro Pete Ya Bada
Published: December 3, 2025 at 8:42 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 4, 2025

‘Yan majalisun dokokin tarayya a nan Amurka su na kara zafafa neman binciken sakataren tsaro Pete Hegseth, dangane da wani lamari na bude wuta a karo na biyu a kan wani jirgin ruwan da aka kai ma farmaki daga farko, matakin da idan ya tabbata zai zamo abinda ya karya dokar yaki da kuma dokokin Amurka.

Sanata Roger Wicker, dan jam’iyyar Republican daga Jihar Mississippi, kuma shugaban kwamitin kula da harkokin soja na majalisar dattijai, yace wannan zargi ne mai karfi, kuma shine dalilin da ya sa tilas su gudanar da bincike.

Jiya talata, Hegseth ya kare hari na biyu da aka kai kan wannan jirgin ruwa, yana mai cewa rashin kyawun yanayi a lokacin kai harin na farko shi ya janyo hakan, yana mai cewa wuta da hayaki sun tashi a lokacin harin na farko kuma shi bai ga wani wanda ya tsira da rai ba a lokacin da aka bada umurnin sake bude wuta a kan jirgin ruwan.

Amma ana samun karin ‘yan majalisar dokoki daga dukkan jam’iyyu biyu da kuma kwararru kan harkokin soja dake fadin cewa harin na ranar 2 ga watan Satumba, matakin soja ne na haramun.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu
Next Post: Za’a Dauko Messi Aro Zuwa Barcelona Deco

Karin Labarai Masu Alaka

Tsananin Sanyi Ya Kashe Mutane 38 A Amurka Amurka
Iran Da Amurka Zasu Cimma Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni Afrika
Kungiyar ISIS Ta Kashe Sojojin Amurka Biyu Amurka
Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa Amurka
Iran Ta Kama Wasu ‘Yan Leken Asiri Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana Amurka
  • Kasashen Amurka Da China Sun Matsawa Ghana Domin Rage Kudaden Haraji Afrika
  • Ukraine Ta Aika Tawagar Kwararru Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne Amurka
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Gyara Dokar Kasafin Kudi Labarai
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji A Kauyen Wanka Jihar Filato Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Wajen Hakar Ma’adanai Dake Jihar Filato Najeriya
  • Shugaba Tinubu Ya Turawa Majalisa Sunayen Mutane Biyun Da Zasu Shugabanci Sashin Albarkatun Mai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.