A hudubar Kirsimetinsa ta farko a yau alhamis, Paparoma Leo, ya nuna jimamin hali da al’ummar Falatsinu suke ciki a yankin zirin Gaza, yana mai furta cewa ta yaya mai hankali zai kalli Falasdinawan dake zaune cikin tanti, inda suka yi makonni suna fama da ruwan sama da iska da kuma sanyin hunturu.
Paparoma Leo, wanda shine ba Amurke na farko da aka taba zaba Paparoma a watan Mayu, wanda kuma wannan shine kirsimetinsa na farko a kan wannan mukami, bai saba fitowa yana magana kan batutuwan siyasa a hudubarsa ba.

Sabon Paparoman ya sha yin maganganu a kan halin da Falasfinawa suke ciki a Gaza, inda a watan da ya shige ya fadawa ’yan jarida cewa hanya daya tak ta kawo karshen takun sakar da aka jima ana yi a tsakanin Isra’ila da Falasdinawa ita ce ta kafa kasar Falasdinu.
Haka kuma Paparoma Leo ya nuna jimamin halin da ‘yan gudun hijira suke ciki a nahiyar Amurka, Paparoman wanda can baya ya sha sukar shugaba Donald Trump na Amurka game da matakan da yake dauka a kan ‘yan gudun hijira, bai ambaci sunan shugaban a hudubar tasa ta yau ba.
Amma a hudubar da yayi ta jajiberin kirsimeti a ranar laraba, Paparoman ya ce kin taimakawa talakawa ko baki, tamkar kin bin umurnin Allah ne.


