Gwamnatin kasar Malawi tace a yau Alhamis a kalla mutane 13 ne suka rasa rayukan su bayan da aka shafe kwanaki 4 ana tafka ruwan sama da yayi sanadiyyar ambaliyar ruwa a fadin kasar.
Ma’aikatar kula da ayyukan agajin gaggawa da matsalolin ibtila’i tace ta samu rahotanni daga 16 cikin 36 na majalisun kasar. Zuwa yanzu ambaliyar ruwan ya shafi gidaje 9,598, an kuma kafa sansanoni a majalisu 6, yayain da ma’aikatar bada agaji ta fara raba kayan tallafi ka magidantan da abun ya shafa.
Kasar na neman taimako daga ‘yan kawancen ta na gida da na kasashen waje yayin da ake ci gaba nema tare da kubutar da mutanen da abun ya shafa.


