Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya
Published: December 11, 2025 at 6:49 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kwamitocin Kasafin Kuɗi na Majalisar Dokokin Amurka sun jaddada kudirin Amurka na tunkarar take-taken addini a duniya, musamman a Najeriya.

Wannan na zuwa ne bayan ziyarar tawagar ‘yan majalisar da Shugaba Donald Trump ya tura ƙarƙashin jagorancin Riley Moore.

A Najeriya, tawagar ta gana da mai bawa Shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, domin ƙarfafa haɗin gwiwar yaki da ta’addanci da tsaro a yankin.

Moore ya kai ziyara Benue, inda ya gana da shugabannin Katolika da na al’ummar Tiv tare da duba sansanonin ‘yan gudun hijira.

Ya bayyana abin da ya gani a matsayin abin tausayi, inda ya ruwaito tashin hankali da kisan gilla da suka tilasta dubban Kiristoci tserewa daga gidajen su.

Ya ce fiye da Kiristoci 600,000 na rayuwa a sansanonin ‘yan gudun hijira a Benue. Moore ya kuma yi zargin “harin kisan kare dangi da Fulani suke yi a jihar.

Tawagar ta yaba wa gwamnatin Najeriya kan ceto daliban makarantar Katolika fiye da 100, tare da cewa ƙawancen tsaro tsakanin Najeriya da Amurka ya fara inganta, amma akwai sauran aikin da za a yi.

Ziyarar ta zo ne a daidai lokacin da dangantaka ke ƙara tsami bayan gwamnatin Trump ta sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake zargin suna keta ‘yancin addini, matakin da ya haddasa ce-ce ku-ce a bangaren diplomasiya.

Gwamnatin Tarayya ta ce ba a nuna bambanci ga addini, saboda rashin tsaro yana shafar kowa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar
Next Post: Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa

Karin Labarai Masu Alaka

Kotu Ta Bada Belin Kwamishinan Kudin Jihar Bauchi Najeriya
Matsalolin Masarautun Kano Sun Kawo Karshe Najeriya
Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
Masarautar Borgu a Jihar Neja na neman daukin Gwamnatin Najeriya akan matsalar rashin tsaro Najeriya
FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya Najeriya
Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mataimakin Gwamnan Bayelsa Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • An Bude Gasar Kwallon Kafa Ta Mata A Najeriya NWFL 2025 Wasanni
  • PDP Zata Karbi Mulki 2027 Inji Shugabannin Jam’iyar Siyasa
  • ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji Afrika
  • Masu Ruwa da Tsaki akan Lamurran Siyasa sun Fara Maida Martani akan Matakin da Ministan Labaran Nigeria da wayar da kan Jama,a Idris Malagi na korar Daya Daga cikin Ma,aikatansa Saboda dalilai na Siyasa. da tsakiayar ranar Wannan larabace dai Mataimakin na Musamman akan yada Labarai ga Minista Malagi Malam Rani,u Ibrahim ya fitar da Wata sanarwar cewa Ministan ya Dakatar da Daya Daga cikin Ma,aikatansa Mai Suna Sa,idu Enagi Saboda ya fitar da Wani bayani a Kafar yada Labarai na sada zumunta dake Nuna Ministan ya shirya tsaf Domin takarar Gwamnan Jihar Neja a 2027. Malam Sa,idu Etsu Tsohon Dantakarar Shugaban cin Jam,iyyar APC a Nigeria Yace Matakin da Ministan ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu lokaci baiyi ba..ceu.. Shima Dattijon Siyasa a Jihar Neja Alh.Awaisu Giwa Kuta Yace Matakin da Ministan Labaran ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu Jihar Neja zaman Makoki Ake na fotinar Yan ta,adda ba wai Batun Neman Mukamin Siyasa ba..ceu .in.. To Sai jigon Jam,iyyar PDP Mai Adawa a Nigeria Hon.Yahaya Ability Yace Akwai kuskure Babba da Ministan ya tabka a dai dai Wannan Zamani na Siyasa duk da cewa Jihar Nejan na cikin Yanayi na masifar Yanbindiga..ceu..in .. Azaben Shekara ta 2023 Malagi ya kara yayi Takara Gwamnan Jihar Neja a jam,iyyar APC inda Gwamna Umar Bago ya kadashi a zaben fidda Gwani.
    Martanin Wasu ‘Yan Najeriya Ga Ministan Labarai Bisa Korar Dadiminsa Najeriya
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani Afrika
  • Afirka Ta Kudu Ta Samu Rigakafin Cutar Boro Afrika
  • Wasu Yara 50 Sun Kubuta Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai
  • An Hana Yada Rahotannin Siyasa A Kasar Uganda Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.