Madugun aikin korar bakin haure a gwamnatin shugaba Donald Trump, ranar talata ya gana da gwamnan jihar Minnesota Tim Watz, bayan da ya karbi jagorancin Gudanar da shirin korar ‘yan gudun hijira ko bakin haure na babu kama hannun yaro a birnin Minneapolis, yayin da fadar White House take kokarin sassauta irin bacin rai da Amurkawa a duk fadin kasar suka nuna, bayan da jami’an hukumar shige da fice suka kashe ba Amurke na biyu cikin watan nan a birnin na Minneapolis.
A cikin wata sanarwa da tashar talabijin din CNN ta ruwaito, gwamna Waltz yace jihar ta bayyana wa Homan muradun ta da suka hada da gudanar da bincike babu son rai kan kisan mutanen nan biyu, da kuma rage jami’an aikin shige da fice su dubu uku da gwamnatin tarayya ta tura zuwa birnin na Minneapolis. Sanarwar tace, Homan da Waltz sun amince zasu ci gaba da aiki tare domin cimma wannan buri.
Matakin gwamnatin Trump na tura Homan ya maye babban jami’in aiki shige da fice Gregory Bovino, ya biyo bayan damuwar da mukarraban shugaban na Amurka suka nuna cewa kashe Alex Pretti dan shekaru 37 da haifuwa yana iya gurgunta shirin gwamnatinsa kan bakin haure.


