Bahrain ta gabatar da wani daftarin kuduri na kwamitin sulhu na MDD, da zai baiwa kasashen ikon suyi amfani da duk wani mataki da ya wajaba, wajen kare zirga zirgar jirage a mashigin ruwan Hormuz, daftari da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya gani.
Jami’an difiomasiyya suka ce daftarin ya samu goyon bayan wasu kasashen da suke yankin Gulf, tareda Amurka, duk da haka sun nuna shakkun daftarin ba zai sami amincewa ba.
Matakin yana nuna karin damuwa a yankin, cewa Iran zata ci gaba da barzana ga mashigin ruwan na Hormuz, domin ta nan ne ake jigilar kashi 20 cikin dari na mai da iskar Gas da duniya take amfani dashi, wanda kuma shine karfin tattalin arzikin da kasashe da suke yankin.


