Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11
Published: December 18, 2025 at 7:17 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Burkina Faso ta saki mayakan Najeriya su 11 wadanda ta tsare fiye da mako guda da ya shige, a bayan da jirginsu yayi saukar gaggawa.

Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar, ya fada ranar alhamis cikin wata sanarwa ta kafar X cewa an warware batun matuka jirgin saman yakin Najeriya da mutanen dake cikin jirgin ta hanyar diflomasiyya.

Sanarwar ta ce gwamnatin mulkin soja ta Burkina Faso a karkashin jagorancin Ibrahim Traore, ta sako sojojin saman a bayan ganawa da wata tawagar Najeriya karkashin jagorancin Tuggar.

A makon da ya shige rundunar mayakan saman Najeriya ta ce jirgin yana kan hanyarsa ta zuwa kasar Portugal domin sabis da aka saba yi ma jirage a lokacin da yayi saukar gaggawa a garin Bobo Dioulasso a yammacin Burkina.

Amma kuma gidan talabijin na kasar Burkina Faso ya watsa wani jawabin ministan harkokin wajen Najeriya Tuggar ranar laraba, inda yake cewa an bi ta hanyoyin da ba su dace ba wajen neman izinin wucewar jirgin ta samaniyar kasar, ya kuma nemi ahuwar hakan.

Shugaban gwamnatin mulkin soja ta kasar Mali, Janar Assimi Goita, ya ce saukar gaggawar da jirgin na Najeriya yayi, ya sa Kungiyar Kasashen Yankin Sahel ta sanya dakarun tsaron samaniyarta cikin shirin ko ta kwana, tare da ba su iznin harbo duk wani jirgin da ya shiga samaniyar yankin ba tare da izni ba.

Wannan kungiya ta kunshi kasashen Mali, Burkina Faso da Jamhuriyar Nijar.

Ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta ce a yanzu matuka jirgin saman zasu wuce da shi wurin gyara a kasar Portugal.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC
Next Post: Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa

Karin Labarai Masu Alaka

NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas Najeriya
Za A Rantsar Da Mainasara Kogo A Matsayin Shugaban Kundin Da’ar Ma’aikata Labarai
Rikici Ya Barke A Kano Bayan Kashe Wani Matashi Da Ake Zargi Da Kashe Ladani Najeriya
Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma Labarai
Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba Kiwon Lafiya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno
  • A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela
  • Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku
  • Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma
  • Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Gobara Mafi Muni Cikin Shekaru 60 A Hong Kong Ta Hallaka Rayuka Sauran Duniya
  • Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai
  • Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA. Labarai
  • Hukumar Tsaro Ta DSS Ta Aika Sammaci Dr. Yusuf Baba-Ahmed Labarai
  • Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
  • Burkina Faso: Mun Kama Sojojin Najeriya da Jirgin Yaki Bisa Shigowa Ba Bisa Ka’ida Ba Afrika
  • Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.