Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025
Published: January 29, 2026 at 8:05 AM | By: Bala Hassan

Hukumar ladabtarwa ta CAF ta kakabawa hukumar kwallon kafa ta Senegal FSF, da hukumar kwallon ta Moroko takunkumi.

Hukumar ladabtarwa ta (“CAF”) ta sanya takunkumi kan Senegal da Moroko da wasu ‘yan wasa da jami’ai game da abubuwan da suka faru a lokacin gasar cin kofin Afirka na CAF na Moroko 2025, wanda ya keta ka’idojin CAF.

Hukumar ladabtarwa ta CAF ta dauki matakai kamar haka:

Game da Hukumar Kwallon Kafa ta Ƙasar Senegal (FSF), Hukumar Ladabtarwa ta CAF ta yanke shawarar dakatar da Mr Pape Bouna Thiaw, Babban Kocin Kungiyar Kwallon Kafa ta Senegal, na wasanni biyar (5) Wacce CAF ta shirya saboda rashin da’a da a wasan karshe wanda ya saba wa ka’idojin dokar CAF da kuma kawo rashin mutunta wasan an kuma ci Pape Bouna Thiaw tarar dalar Amurka 100,000.

Bayan haka CAF ta dakatar da dan wasan Senegal, Iliman Cheikh Baroy Ndiaye na wasanni biyu (2) na CAF, saboda rashin da’arsa ga alkalin wasa, CAF ta dakatar da dan Senegal, Ismaila Sarr na wasanni biyu (2) na CAF shima saboda rashin da’a da ya yi wa alkalin wasa.

Ita ma hukumar kwallon kafa ta Ƙasar Senegal (FSF), an ci tararta dala 300,000 saboda rashin da’a da magoya bayanta, suka nuna a ranar wasan wanda ya karya ka’idojin CAF na yin wasa mai kyau da mutunci, da kuma karin tarar dala 300,000 saboda rashin da’a daga ‘yan wasansu da ma’aikatan horaswa wanda CAF ta bayyana shi a matsayin rashin mutunta wasan.

Akwai tarar ga (FSF), dala 15,000 saboda rashin da’a na kungiyarta ta Ƙasar, saboda biyar (5) cikin ‘yan wasanta sun sami gargadi.

A bangaren Hukumar Kwallon Kafa ta Ƙasar Moroko (FRMF), Hukumar Ladabtarwa ta CAF ta yanke shawarar

dakatar da dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Moroko, Achraf Hakimi na wasanni biyu (2) na hukumar CAF, tare da dakatar da wasa daya (1) na tsawon shekara daya (1) daga ranar da aka yanke wannan hukunci, saboda rashin da’a da ya yi a wasan, bayan haka CAF ta dakatar da dan wasan kungiyar kwallon kafa na Moroko Ismaël Saibari wasanni uku (3) na hukumar CAF shima saboda rashin da’arsa an kuma ci Ismaël Saibari tarar dala 100,000.

CAF ta kuma ci tarar hukumar kwallon kafa ta Ƙasar Moroko (FRMF) dala 200,000, saboda rashin da’ar ‘yan wasan a filin wasa a lokacin wasan karshe na kofin kasashen Afirka AFCON 2025.

Da kuma karin tarar dala 100,000 saboda rashin da’a na ‘yan wasanta da ma’aikatan horaswa, waɗanda suka mamaye duba VAR suka kuma hana aikin alkalin wasa, wanda ya saɓa wa ƙa’idodin yin wasa sashe na 82 da 83 na Dokar Ladabtarwa ta CAF.

A kwai kuma tarar da aka ci Hukumar Kwallon Kafa ta Moroko (FRMF) dala 15,000 saboda amfani da na’urorin laser da magoya bayanta suka yi a lokacin wasan aikata haka laifine.

Dangane da korafin kan Hukumar Kwallon Kafa ta Moroko (FRMF) ta shigar kan zargin keta dokoki daga Hukumar Kwallon Kafa ta Senegal (FSF) inda ta bukace a kwace kofin bisa sashe na 82 da 84 na Dokokin Gasar Cin Kofin Afirka kuwa

hukumar Ladabtarwa ta CAF ta yi watsi da wannan korafin da Hukumar Kwallon Kafa Moroko (FRMF) ta shigar kan Senegal (FSF).

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Maganganun Jami’an Shige Da Fice Dana Shugaban Kasa Trump Suna Cin Karo Da Juna
Next Post: Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Biyan Hakkokin Tsofin Ma’aikata 800

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida Afrika
Thailand Da Cambodia Sun Fara Tattauunawa Kan Batun Tsagaita Wuta Labarai
Kyaftin Na Super Eagles Ya Yi Ritaya. Wasanni
Ba Shakka Najeriya Zata Iya Shiga Gasar Harbi Ta Duniya Wasanni
AFCON ChelIe, Ya Fidda Sunayen ‘Yan Wasan Super Eagles Na Karshe. Wasanni
Wakilan Rasha Da Ukraine Sun Tattauna A Abu Dhabi Ranar Juma’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Soke Bashin Da Gwamnati Take Bin NNPC Najeriya
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • EFCC Ta Cafke Fitacciyar Jarumar Kannywood Samha Inuwa Labarai
  • Anyi Rashin Mutane Da Yawa Yayinda Bom Ya Fashe Ana Sallar Magariba Maiduguri Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Ta Tura Mutane 386 Gidan Yari Afrika
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria Siyasa
  • Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka
  • Amurka Da Iran Sun Tattauna A Kasar Pakistan Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.