An Bude Makarantu A Najeriya
An fara bude makarantu a fadin wasu sassan arewacin Najeriya ranar Litinin, bayan watanni da rufe makarantun, sakamakon sace daruruwan dalibai a cikin watan Nuwamban bara. Sace sacen daliban a bara ya nuna irin matsalolin tsaro da sashen ilmi yake fuskanta a yankin da yake fama da fitinar kungiyoyi barayi da mayakan sakai dake ikirarin…

