Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

CBN: An Samu Ƙaruwar Masu Cin Bashin Banki Basa Biya
Published: January 20, 2026 at 4:42 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Bankuna a Najeriya sun bayar da rahoton karuwar rashin biyan bashi a daga magidanta da kamfanoni duk da cewa samuwar rance da bukatar sa sun karu, a cewar binciken yanayin bashi na babban bankin Najeriya (CBN) na zangon karshe na 2025.

Rahoton ya nuna cewa rashin biyan bashi ya karu a dukkan nau’ikan rance, ciki har da rancen dake da jingina da wanda bai da jingina, da kuma na kamfanoni.

Kananan gidaje da kamfanoni kanana sun fi fuskantar matsala saboda hauhawar farashi, tsadar makamashi, da karancin kudin shiga.

A bangaren manyan kamfanoni, rashin biyan bashi ya kai kashi 6% a wasu lokuta, yayin da sauran kamfanonin kudi suka samu matsakaicin rashin biyan bashi na kashi 6.2%, lamarin da ke nuna tsanani a bangarorin tsarin kudi.

Duk da haka, bankuna sun kara bayar da rance ga gidaje da kamfanoni, amma babban bankin Najeriya ya yi gargaɗin cewa karuwar rashin biyan bashi na iya lalata ingancin kadarori da rage karfin bankuna.

CBN ta kuma ba da shawarar inganta tsarin dawo da bashi da kiyaye ka’idojin banki don rage matsalar.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tinubu Ta Karyata Kafa Kamfanin Gwal A Legas
Next Post: Hukumar NAHCON Ta Kamallah Shirye Shiryen Hajjin 2026 A Kasar Saudiya

Karin Labarai Masu Alaka

Sarkin Musulmi Ya Ziyarci Shugaba Bola Tinubu Afrika
Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000 Najeriya
Ga Fili Ga Doki Najeriya
NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai Afrika
Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya
‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Biyan Hakkokin Tsofin Ma’aikata 800 Labarai
  • Tsofin Ma’aikatan Gwamnati Sunyi Zanga Zanga A Jihar Neja Labarai
  • Rasha Takai Mummunan Hari Birnin Kyiv Afrika
  • Makiyaya Sun Shiga Matsala Sakamakon Fari A Kasar Kenya Afrika
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg Afrika
  • Tsohon Shugaban Brazil Bolsanaro Zai Tafi Gidan Yari Labarai
  • ‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi Afrika
  • Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.