Cibiyar Carter, wadda tsohon shugaban kasar Amurka Jimmy Carter tare da mai dakin sa suka kafa, don tallafawa walwalar al’umma ta ko wanne fanni ta sanar cewa a shekarar 2025, mutane 10 ne kacal aka samu masu dauke da cutar kurkunu, kuma sun fito ne daga kasashe 3.

Wannan sakamakon ya biyo bayan kasa da shekara daya na rasuwar Jimmy Carter, wanda yayi fatan yaga karshen cutar kafin ya mutu. A lokacin da cibiyar Carter ta kaddamar da shirin kawar da cutar kurkunu a shekarun 1980, sannan miliyoyin mutane na kamuwa da cutar a kasashe masu tasowa.
Amma ya zuwa shekarar 2025, an samu masu dauke da cutar 4 a Chadi, 4 a Habasha, sannan kuma aka samu 2 a Sudan ta Kudu kacal.


