Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Dalibai Sun Koma Makarantu A Wasu Jihohin Najeriya
Published: January 13, 2026 at 12:45 PM | By: Mustapha Nasiru Batsari | Updated: January 13, 2026

Bayan shafe makonni bakwai suna hutun dole, daliban makarantun firamare da sakandare a jahar filato sun koma azuzuwa don ci gaba da neman ilimi.

Rufe makarantun da gwamnatin jahar Filato ta yi a watan Nuwamban bara, ta ce ta yi ne don yin rigakafi, sakamakon matsalolin tsaro da garkuwa da dalibai da ‘yan bindiga suka yi a wassu jihohin Najeriya,
Wassu daliban firamare na makarantar gwamnati ta Obasanjo Model School dake Jos, Favour Francis Daniel da Yane Iliya Bulus Choji sun bayyana yadda zasu tinkari jarabawa bayan dawowarsu daga hutun dole.

Shugaban sashen makarantar Obasanjo Model School Jos, Mangai Obi Maren yace yayi farinciki da daliban suka dawo a ranar farko.

Da shike tun farko gwamnati ta rufe makarantun ne saboda tsaro, na garzaya ofishin shirin samadda tsaro a makarantun jahar Filato.

Daraktan tsare-tsare na shirin, Mr Ben Chikan yace gwamnati ta hada kai da masu ruwa da tsaki don samadda tsaro a makarantun jahar.
Sakatare a hukumar ilimin bai daya matakin farko a jahar Filato, Tang’an Emmanuel yace ya zaga makarantun ya kuma ga yadda malamai da dalibai suka dukufa wajen koyo da koyarwa.

Jihohi tara ne a fadin Najeriya suka rufe makarantu a watan Nuwamban dubu biyu da ishirin da biyar, yayinda gwamnatin tarayya ta rufe makarantun unity arba’in da bakwai a fadin kasar, wanda a yanzu kudan dukkan jihohin sun umurci dalibai su koma makarantu, in banda jahar Edo da ita ma ta umurci makarantun su kasance a rufe saboda matsalolin tsaro.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/DALIBAI-SUN-KOMA-MAKARANTU-1.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Anfara Tantance Lafiyar Maniyyatan Jihar Gombe
Next Post: Kasar Gambiya Ta Gayawa Kotun MDD Shirin Myanmar Akan Musulmai

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
Jihar Gombe Ta Saka Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanonin Tunisiya Kimiya
Shugaba Tinubu Ya Isa Legas Domin Hutun Karshen Shekara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe Najeriya
CBN: An Samu Ƙaruwar Masu Cin Bashin Banki Basa Biya Najeriya
An Yiwa Dokokin Kare Hakkin Yara Rikon Sakainar Kashi Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • INEC Mayar Da Lokacin Zaɓen 2027 Kafin Azumi Najeriya
  • Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji Najeriya
  • Farashin Danyen Mai Ya Farfado Fiye Da Kashi Daya Sauran Duniya
  • Senegal Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirka Afcon 2025. Wasanni
  • Kasar Namibiya Tayi Watsi Da Yarjejeniya Tsakanin Ta Da Kamfanin Total Labarai
  • Maharan Bindiga Sun Kashe Mutane 12 Masu Hakar Ma’adanai A Jihar Filato Labarai
  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno Tsaro
  • Shin Ko Ganawar Zelensky Da Macron Zata Haifar Da ‘Da Mai Ido? Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.