Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Dalibai Sun Koma Makarantu A Wasu Jihohin Najeriya
Published: January 13, 2026 at 12:45 PM | By: Mustapha Nasiru Batsari | Updated: January 13, 2026

Bayan shafe makonni bakwai suna hutun dole, daliban makarantun firamare da sakandare a jahar filato sun koma azuzuwa don ci gaba da neman ilimi.

Rufe makarantun da gwamnatin jahar Filato ta yi a watan Nuwamban bara, ta ce ta yi ne don yin rigakafi, sakamakon matsalolin tsaro da garkuwa da dalibai da ‘yan bindiga suka yi a wassu jihohin Najeriya,
Wassu daliban firamare na makarantar gwamnati ta Obasanjo Model School dake Jos, Favour Francis Daniel da Yane Iliya Bulus Choji sun bayyana yadda zasu tinkari jarabawa bayan dawowarsu daga hutun dole.

Shugaban sashen makarantar Obasanjo Model School Jos, Mangai Obi Maren yace yayi farinciki da daliban suka dawo a ranar farko.

Da shike tun farko gwamnati ta rufe makarantun ne saboda tsaro, na garzaya ofishin shirin samadda tsaro a makarantun jahar Filato.

Daraktan tsare-tsare na shirin, Mr Ben Chikan yace gwamnati ta hada kai da masu ruwa da tsaki don samadda tsaro a makarantun jahar.
Sakatare a hukumar ilimin bai daya matakin farko a jahar Filato, Tang’an Emmanuel yace ya zaga makarantun ya kuma ga yadda malamai da dalibai suka dukufa wajen koyo da koyarwa.

Jihohi tara ne a fadin Najeriya suka rufe makarantu a watan Nuwamban dubu biyu da ishirin da biyar, yayinda gwamnatin tarayya ta rufe makarantun unity arba’in da bakwai a fadin kasar, wanda a yanzu kudan dukkan jihohin sun umurci dalibai su koma makarantu, in banda jahar Edo da ita ma ta umurci makarantun su kasance a rufe saboda matsalolin tsaro.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/DALIBAI-SUN-KOMA-MAKARANTU-1.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Anfara Tantance Lafiyar Maniyyatan Jihar Gombe
Next Post: Kasar Gambiya Ta Gayawa Kotun MDD Shirin Myanmar Akan Musulmai

Karin Labarai Masu Alaka

Akwai Alamar Shawarwari Tsakanin Amurka Da Turai Zai Kawo Karshen Yakin Rasha Amurka
Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas Najeriya
Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Shugaba Bola Tinubu Ya Tafi Turai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu Sauran Duniya
  • Gangamin Wayar Da Kai Don Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Jihar Gombe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shirin Manuniya Kashi Na Daya, Yau Juma’a 11.21.25 Shirye-Shirye
  • Alaka Na Cigaba Da Kamari Tsakanin Rwanda Da Barundi Labarai
  • Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Rivers: ‘Yan Majalisa 16 Sun Canza Sheka Zuwa APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamna Fubara: Rashin Kariya daga PDP Ne Ya Tilasta Ni Komawa APC Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.