Wata gobara da ta tashi a ranar Litinin ta ƙone ajujuwan karatu 34 a wata makarantar kiwon lafiyar dabbobi da ke karamar hukumar Kabo a jihar Kano.
A cewar wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar kashe gobara ta ta Jihar Kano, ACFO Saminu Yusif Abdullahi, ya fitar, ya ce lamarin ya faru da misalin ƙarfe 2:53 na rana.
Sanarwar ta ce dakin kula da gobara na hukumar ya karɓi kiran taimako daga wani Jamilu Abubakar, wanda ya ba da rahoton tashin gobara a cikin makarantar. Nan da nan aka tura ma’aikatan kashe gobara daga tashar Rijiyar Zaki zuwa wurin da lamarin ya faru.
“Da suka iso wurin, ma’aikatanmu sun gano wani ginin bene na ƙasa mai fadin ƙafa 500 da tsayin ƙafa 500, da ake amfani da shi a matsayin wajen kiwon lafiyar dabbobi, yana ƙonewa cikin wuta,” in ji sanarwar.
Sanarwar ta ƙara da cewa dakuna 16 sun lalace sosai, yayin da wasu 18 suka samu lalacewar ɓangare-ɓangare saboda gobarar.
Sai dai an samu nasarar dakile wutar, inda aka hana ta yaɗuwa zuwa sauran dakuna da ofisoshi a cikin cibiyar.
“An tura motar kashe gobara guda ɗaya daga tashar Rijiyar Zaki don dakile lamarin, in ji sanarwar, wadda ta danganta nasarar aikin da saurin martanin ma’aikatan kashe gobara.
Ba a samu rahoton mutuwar kowa ba a lokacin da ake rubuta wannan rahoto, yayin da ba a bayyana musabbabin gobarar ba.


