Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka
Published: December 23, 2025 at 2:29 AM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 23, 2025

Wasu jami’an tsaron Najeriya sun bada tabbaci ga ‘yan kasar cewa babu wani abun tashin hankali ko fargaba gameda jiragen leken asiri na Amurka da suke shawagi a sararrin samaniyar kasar. Suka ce matakin ya faranta musu rai saboda Amurka tana taimakawa Najeriya ne ta fuskar tsaro.

Jami’an tsaron sun tabbatarwa Amurka Ke Magana cewa matakin na hadin gwiwa ne tsaknin jami’an tsaron Amurka da mayakan sama na Najeriya. Suka ce akwai sojojin sama na Najeriya a cikin jiragen da suke aikin leken asirin a sararin samaniyar kasar.

Jiragen suna tashi ne daga Ghana. Wannan matakin ya biyo bayan shawarwari da jami’an gwamnatin Najeriya suka yi da gwamnatin Amurka, bayan da shugaban Amurka Donald Trump, yayi barazanar kai hari kan Najeriya domin kare kiristocin kasar wadanda ake zargin ana yi musu kisn kare dangi. Gwamnatin Trump ta amince zata taimaki Najeriya ne bayan da aka gabatar mata da irin kalubale da kasar take fuskanta ta fuskar tsaro.

Gameda zargin gwamnatin Najeriya tana biyan kudin fansa kamin a saki mutane da ake garkuwa da su, musamman dalibai daga makarantu da ‘yan bindiga suke sace su, jami’an tsaron sun rantse da Allah cewa babu sisin kwabo daga aljihun Najeriya da yake fita domin biyan kudin fansa.

Daga nan suka yi kira ga ‘yan Najeriya su daina yi wa matakan gwamnati bahaguwar fahimta, maimakon haka a kullum su bukaci bayani, kamin su yanke shawara kan batu da  ya shafi gwamnati da al’uma.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya buga labarin zirga-zirgar jiragen leken asirin  sararin samaniyar Najeriya.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: An Samu Nasarar Karbo Karin Yara 130 Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda
Next Post: Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta

Karin Labarai Masu Alaka

Majalisar Wakilai Tayi Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Gombe Labarai
Motar Kungiyar Kwallon Kafar Bayelsa United Ta Yi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Mace Ta Farko Da Zata Shugabanci Jami’ar Northwest Dake Kano Najeriya
Barau Jibril: Mu Ba ‘Yan Amshin Shata Bane A Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango Afrika
  • Harin Makami Mai Linzami Da Rasha Ta Kai Yayi Barna Sosai A Ukraine Afrika
  • An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Don Neman Zaman Lafiya Labarai
  • ‘Yan Kasar Venuzuela Zasu Fara Komawa Gida Amurka
  • Masar Tayi Yarjejeniyar Makamashi Da Kasashen Norway Da China Labarai
  • Venezuela Ta Sako Karin Mutanen Da Take Tsare Dasu Labarai
  • Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya Afrika
  • Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.