Jihar Gombe ta yi fice a gasar kiwon lafiya a Matakin farko ta ƙasa ta 2025, ta lashe Dalar Amurka 400,000
Jihar Gombe ta sake tabbatar da jajircewarta wajen inganta harkar kiwon lafiya, inda ta samu matsayi na biyu a shiyyar Arewa Maso Gabas a gasar Jagorancin Kiwon Lafiya Matakin Farko (PHC Leadership Challenge) ta shekarar 2025, tana yin fintinkau kan jihohi shida na shiyyar.
Sakamakon wannan ƙwazon da Gombe ta nuna wajen ƙarfafa tsarin kiwon lafiyar farko, an karrama ta da kyautar dala 400,000.
An miƙa kyautar ne yayin bikin karramawa na 2025 PHC Leadership Challenge da aka gudanar a cibiyar taro ta Bola Ahmed Tinubu, dake Abuja.
Bikin ya samu halartar manyan jami’ai da masu ruwa da tsaki a fannin lafiya, inda mataimakin shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya jagoranci taron.
A shekarar da ta gabata ma, jihar Gombe ta kafa tarihi inda ta lashe PHC Leadership Challenge Innovation Award, lambar yabo ta kirkira da aka fara bayarwa tun bayan ƙaddamar da shirin, kuma ta zama ta biyu a Arewa Maso Gabas, lamarin da ya kawo mata kyautar dala $400,000.
Wannan ci gaba ya sake tabbatar da cewa Gombe na kan gaba wajen inganta harkar kiwon lafiya na asali a Najeriya.


