An ceto mutum daya da ransa, ana kuma fargabar wasu 50 sun halaka, lokacin da karamin jirgin ruwan da suke ciki ya nuste a tekun miditerennean, ba nisa daga gabar ruwa a Tunisia, kamar yadda jami’ai suka fada a ranar lahadi.
Mutumin yayi s’o’i 24 cikin ruwa, kuma ya ce yana jin babu wani daga cikin jirgin da yake ciki da ya tsira, kamar yadda wata kungiyar mai rajin kare hakkin ‘yan gudun hijira da ake kira Alarm Phone Group ta fada.
Kungiyar tace jirgin ya taso ne daga Tunisa, wadda kamar yadda Kungiyar tace wurin tashin ‘yan gudun hijira ne wadanda suke kasadar yin tafiya mai hadari da nufin kai wa turai.
Wani babban jirgin ‘yan kasuwa ne ya ceto mutumin ya kai shi Malta domin jinya, kamar yadda Sojojin Maltan suka fada. Duka sojojin, da kuma ita Kungiyar kare hakkin ‘yan gudun hijra Alarm Phone Group ba su fadi lokacin da aka ceto mutumin ba.


