Hukumar kula da kasuwannin zuba jari ta Ghana, ta umarci kamfanonin saye da sayar da hannayen jari a kasar su rage zuba jari a kasashen waje, a kokarin da take yi na kare darajar kudin kasar da ake kira Cedi da samun daidito a harkokin tattalin arzikin kasar.
Ghana wacce babba ce a hako zinari da noman cocoa a duniya, yanzu take farfadowa daga matsanancin yanayi na tattalin arziki data juma bata fada irinsa ba, ana sa ran zata kammala zagaye na uku na mu’amalarta da asusun bada lamuni na duniya da ake kira IMF a takaice cikin watan Agustan bana.
A cikin wata sanarwa data bayar wajajen maraicen ranar jumma’a, hukumar tace nan take hukumar ta haramtawa masu kamfanonin zuba jari amfani da fiye da kashi 20 cikin dari na jarinsu a kasashen waje, yayinda masu zuba jari da ada aka basu damar zuba jari na kachokan kudade da suke hanunsu, yanzu za’a kayyade suyi amfani da kashi 70 cikin dari na kudade da suke dashi.
Hukumar tace, tilas kamfanonin saye da sayar da hannayen jari su zuba jari a kasashen da hukumomi irinta suke musayar bayanai da ita hukumar ta Ghana.


