Kasashen da suke yankin Gulf da farko ba su goyi bayan Amurka ta kai hari kan Iran ba, amma yanzu suna kira da Amurka kada ta dakatar da yakin, ta yadda zata kyale gwamnatin da take Tehran da zata ci gaba da barazana ga kadarorin mai da tattalin arzikin da suka dogara akan su, kamar yadda kamfanin dilancin labarai na Reuters yaji daga majiyoyi uku a yankin na Gulf.
A lokaci daya kuma,wadannan majiyoyi da kuma jakadun kasashen larabawa da suke aiki a kasashen yammacin duniya 5, sunce Washington tana matsawa kasashe da suke yankin Gulf da su shiga yakin da Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan Iran. Kamar yadda uku daga cikin su suka fada, shugaba Trump yana so ya nuna cewa kasashe dake yankin suna goyon bayan yakin, domin hakan zai nuna cewa duniya tana goyon bayan matakin, hakan kuma zai karawa yakin goyo bayan Amurka.
“Akwai tunani a duk fadin yankin Gulf cewa, Iran ta wuce gona da iri kan duk wata kasa dake yankin,” inji Abdulaziz Sager, shugaban wata cibiya mai nazari a Saudiyya, wanda yana sane da irin tunanin gwamnati kan wannan rikici.
“Da farko mun kare su, muka ki goyon bayan yakin,” inji Abdulaziz, “amma da zarar suka fara auna hare haren su akan mu, sun zama makiya. Kuma babu wata hanyar da za’a kalle su.
Ahalinda ake ciki kuma shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana fushinsa kan kasashe da suke yammacin duniya wadanda kawayenta ne, saboda sunyi biris da kiran da yayi na cewa su tura jiragen yaki na ruwa domin su taimaka wajen bude mashigin ruwan Hormuz. Yace Amurka ta tallafa ta kuma kare su, amma ga yanzu yadda suke saka mata. Kasashen Jamus da Japan, da Spain, da Italiya suka ce ba za su tura jiragen su domin tallafawa yakin ahalin yanzu ba.


