Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kasashen Yankin Gulf Sun Bukaci Amurka Takawo Karshen Iran
Published: March 17, 2026 at 4:16 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kasashen da suke yankin Gulf da farko ba su goyi bayan Amurka ta kai hari kan Iran ba, amma yanzu suna kira da Amurka kada ta dakatar da yakin, ta yadda zata kyale gwamnatin da take Tehran da zata ci gaba da barazana ga kadarorin mai da tattalin arzikin da suka dogara akan su, kamar yadda kamfanin dilancin labarai na Reuters yaji daga majiyoyi uku a yankin na Gulf.

A lokaci daya kuma,wadannan majiyoyi da kuma jakadun kasashen larabawa da suke aiki a kasashen yammacin duniya 5, sunce Washington tana matsawa kasashe da suke yankin Gulf da su shiga yakin da Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan Iran. Kamar yadda uku daga cikin su suka fada, shugaba Trump yana so ya nuna cewa kasashe dake yankin suna goyon bayan yakin, domin hakan zai nuna cewa duniya tana goyon bayan matakin, hakan kuma zai karawa yakin goyo bayan Amurka.

“Akwai tunani a duk fadin yankin Gulf cewa, Iran ta wuce gona da iri kan duk wata kasa dake yankin,” inji Abdulaziz Sager, shugaban wata cibiya mai nazari a Saudiyya, wanda yana sane da irin tunanin gwamnati kan wannan rikici.

“Da farko mun kare su, muka ki goyon bayan yakin,” inji Abdulaziz, “amma da zarar suka fara auna hare haren su akan mu, sun zama makiya. Kuma babu wata hanyar da za’a kalle su.

Ahalinda ake ciki kuma shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana fushinsa kan kasashe da suke yammacin duniya wadanda kawayenta ne, saboda sunyi biris da kiran da yayi na cewa su tura jiragen yaki na ruwa domin su taimaka wajen bude mashigin ruwan Hormuz. Yace Amurka ta tallafa ta kuma kare su, amma ga yanzu yadda suke saka mata. Kasashen Jamus da Japan, da Spain, da Italiya suka ce ba za su tura jiragen su domin tallafawa yakin ahalin yanzu ba.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba
Next Post: An Gargadi Kasar Canada Game Da Tura Sojoji Lebanon

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Zata Kara Tura Sojoji Gabas Ta Tsakiya Afrika
Taron Masu Mu’amala Da Kafar Facebook A Kano Afrika
Farashin Mai Yayi Tashin Gwaron Zabi Afrika
Mahaifiyar Nasiru El Rufai Ta Rasu Afrika
Sarkin Gombe Yayin Hawan Tudun Wada Labarai
Zulum Ya Rushe Majalisar Zartarwa Ta Jihar Borno Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tawagar IMF Tana Kasar Kenya Domin Tattauna Bada Lamuni Labarai
  • Farashin Gangar Mai Yayi Gagarumar Fadi A Kasashen Duniya Labarai
  • Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Abba Kabir Yusuf Ya Koma Jam’iyar APC Siyasa
  • Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya Labarai
  • Shugaba Trump Yace Amurka Da Iran Suna Cigaba Da Tattaunawa Amurka
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • Gwamnatin Shugaba Trump Tana Cigaba Da Janye Jakadunta Zuwa Gida Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.