A Faransa masu gabatar da kara sun nemi kotun daukaka kara ta tabbbatar da hukuncin da kotun kasa ta yanke kan jami’an jam’iyyar masu matsanancin ra’ayin rikau, game da almubazzaranci da kudaden tarayyar turai dangane harkokin zabe.
A hukuncin farko da kotu ta yanke a cikin watan Maris na bara, ta zamo babbar koma baya ga siyasar Mari Le Pen, domin ta haramta mata yin takara na tsawon shekaru biyar ba tare da wani bata lokaci ba.
Idan har kotu ta amince da hukuncin farkon, ‘yar siyasar ba zata yi takara a zaben kasar mai zuwa ba, idan kotu ta rage tsawon haramcin ko tayi watsi da haramcin baki daya, to Madam Le Pen zata iya shiga takara a zaben mai zuwa.
A hukuncin da kotu ta yanke a bara, tace Madam Le Pen ce “kanwa-uwar gami,” wajen kitsa yadda za’a sace kudin kungiyar tarayyar turai har milyan hudu na euro, domin amfani da kudaden wajen biyan ma’aikatan jam’iyyar ta a faransa.
Madam Le pen ta fadawa kotu a daukaka karar cewa ita bata san laifi da ita da wasu ‘yan jam’iyyart suka yi ba.


