Rundunar ’Yan Sandan jihar Bauchi, ta sanar da kama mutane takwas bayan wani rikici da ya ɓarke tsakanin ma’aikatan karɓar haraji da masu babur a cikin garin Bauchi.
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Nafiu Habib, ya fitar, lamarin ya faru ne a ranar Juma’a, a kusa da kofar Wunti, wato Wunti Gate, bayan Filin Wasan Abubakar Tafawa Balewa.
Rahotannin sirri sun nuna cewa wani mai babur mai suna Ayuba Abdullahi ya samu rauni bayan da wasu ma’aikatan haraji suka kai masa hari saboda ƙin amincewa da bada haraji sau da dama.
Wannan lamari ya fusata takwarorinsa, inda suka gudanar da zanga-zanga a ofishin ƙungiyarsu da ke Muda Lawal.
Rundunar ’yan sanda daga ofisoshin A, B da C, tare da Operation Restore Peace da Rapid Response Squad, sun gaggauta zuwa wurin, inda suka tarwatsa masu zanga-zangar tare da dawo da zaman lafiya.


