Majalisar dokokin Somalia ta amince da sauya tsarin mulkin kasar da zai karawa wakilai da shugaban kasar wa’adi da zai kai ga jinkirta zaben kasar da shekara daya.
Kasar wacce take fama da rigingimu tun bayan faduwar gwamnatin kama karya ta Siad Barre a 1991, bata da gwamnatin kasa mai karfi, kuma duk da taimakon dakarun kiyaye zaman lafiya na Kungiyar hada kan kasashen Afirka wajen yakar Kungiyar al-shabab mai alaka da al-Qeada, har yanzu ‘yan tawayen suna rike da yankunan kasar masu yawa, kuma tana da karfin kai hare hare kan manyan biranen kasar.
Ranar laraba, wakilai daga majalisar wakilai da ta dattijan kasar su 222 cikin 329 suka kada kuri’a da baki na amincewa da sauya tsarin mulkin kasar da zai karawa kansu da shugaban kasar wa’adi zuwa shekara biyar daga hudu da tsarin mulkin kasar ya tanadar.


