Ranar talata majalisar dattawan Najeriya ta amince da hukumar zabe ta tura sakamakon zabe nan take ta na’ura, mataki da a baya taki amincewa dashi, bayan da ta fuskanci matsin lamba daga kungiyoyin kwadago, kungiyoyin farar hula, da lauyoyi, wadanda suke kokarin ganin sun hana magudin zabe.

A makon jiya wakilan majalisar suka ki amincewa da umarnin a tura sakamakon zabe nan take bayan da aka kidaya kuri’u ta na’ura, mataki da ‘yan gwagwarmayar kawo sauyi a tafarkin zaben kasar suka jima suna goyon bayansa a zaman wata dama na hana yin shishshigi lokacin da ake tara kuri’u da kidaya su.
Matakin kin amincewa wannan kuduri da majalisar tayi da farko ya janyo mata suka tako ina, har ya sanya ‘yan Gwagwarmaya da shugabannin jam’iyun adawa suka yi zanga zanga ranar Litinin a harabar majalisar dokokin kasar, har suka bukaci majalisar dattawan ta bi sahun majalisar wakilai wacce tun farko ta amince da wannan mataki.
An jima ana zargin zabe a Najeriya yana cike da sayen kuri’u, tarzoma, da kuma rudani, inda daga karshe kotuna ne suke ayyana wanda ya sami nasara.
Kasar zata yi zabe ne cikin watan Feburairun shekara mai zuwa, inda ake sa ran shugaba Tinubu zai nemi wa’adi na biyu kuma na karshe.


