Masar ta jibge gogaggun jiragen yaki da basu da matuka da aka fi sani da drones da turanci, daga Turkiyya a wani karamin tashar jirgin sama mai nesa daga kan iyakarta kudu maso yammacin kasar, mataki da yake nuna ana zafafa yakin basasar da ake yi a Sudan, wadda ke nuna cewa makwabciyar Sudan din tana kara shiga cikin rikicin, kamar yadda jami’ai fiye da 10 da masu fashin baki suka fada.
Masar wacce baya ga kogin Nilu da ya hadata da Sudan, tana da iyaka fiye da tsawon kilomita dubu daya da dari biyu da Sudan, tana bada cikakken goyon baya ga sojojin Sudan masu mulkin kasar, a fafatawa da take yi da dakarun wucin gadin kasar da ake kira RSF a takaice.
Masar ta fara sauya matsayarta game da rikicin na Sudan, lokacin da ‘yan tawayen na RSF suka fara samun nasaran kama wurare a yankin Darfur, da suka hada da kama birnin al-Fashir cikin watan Oktoba, inda nan ne wuri na karshe da sojojin Sudan suke da sansani.
A cikin watan Disamba ne Masar tayi gargadin cewa tsaron kasar yana da nasaba sosai da na Sudan. Kuma Masar ba zata amince da duk wani yunkuri da zai kassara diyaucin Sudan ba.


