Ministan harkokin wajen Iran ya gana da shugaban hukumar sa ido kan makamashin nukiliya na Majalisar Dinkin Duniya a Ranar Litinin, kafin ci gaba da tattaunawa tsakanin Iran din da Amurka don shawo kan rikici game da makaman Nukiliya na Iran, inda alamu kadan ke nunawa za’a samu daidaito, ga kuma barazanar daukan matakin soja dake tunkarowa.
A makon da ya gabata ne, fadar Washington ta aike da jirgin ruwa mai dakon jiragen yaki a karo na biyu zuwa gabas ta tsakiya. Ita kuma kasar Iran a yau Litinin ta fara gabatar da atisayen soja a mashigar Hormuz, wanda gabar ruwa ne mai muhimmanci ga kasashen waje, kuma ta nan ake fitar da man fetur daga kasashen larabawa na tekun Fasha, wadanda suke ta rokon a bi hanyar diplomasiyya don kawo karshen rikicin.
Amurka da Iran sun sake zama don tattaunawa kan shirin Iran na nukiliya, wanda fadar Washington da sauran kasashen yamma ke ganin Iran na yi ne don gina makaman nukiliya. Abinda Iran din ta musanta.
Farashin man fetur bai samu wani sauyi mai yawa ba a ranar Litinin, yayin da masu sa hannun jari suke duba yadda tattaunawa tsakanin Iran da Amurka zata shafi kasuwar man, da kuma sa ran da ake na samun karuwar man daga kasashe masu arzikin man fetur na OPEC.


