Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Najeriya Da Amurka Sun Amince Su Haɗa Kai Don Inganta ’Yancin Addini Da ƙarfafa Tsaro A Nijeriya
Published: January 24, 2026 at 11:19 AM | By: Bala Hassan

Gwamnatin Tarayya Najeriya da Amurka sun amince su haɗa kai don inganta ’yancin addini da ƙarfafa tsaro a Nijeriya

Gwamnatocin Tarayya da ta Amurka sun cimma matsaya kan cewa daga yanzu za su haɗa gwiwa don inganta ’yancin yin addini tare da ƙarfafa tsaro a duk faɗin Nijeriya.

Yarjejeniyar ta biyo bayan taron farko na Guruf ɗin Aikin Haɗin Gwiwa na Amurka da Nijeriya wanda aka gudanar a Abuja a ranar Alhamis, 22 ga Janairu, 2026.

An kafa wannan Guruf ɗin Aiki ne sakamakon sanya Nijeriya a matsayin Ƙasa Mai Bada Matukar Damuwa (wato “Country of Particular Concern”) da Shugaban Amurka Donald J. Trump ya yi a ƙarƙashin Dokar ’Yancin Yin Addini ta Ƙasa da Ƙasa (International Religious Freedom Act).

Ta hanyar haɗin gwiwa ta ƙut-da-ƙut, manufofin Guruf ɗin Aikin su ne rage tashin hankali da ake yi wa ƙungiyoyi masu rauni a Nijeriya, musamman Kiristoci, da kuma samar da yanayi mai kyau da zai ba dukkan ’yan Nijeriya damar yin addinin su cikin ’yanci ba tare da cikas daga ’yan ta’adda, ’yan a-ware, ’yan fashi da makami, da ƙungiyoyin ’yan bindiga ba, ko kuma duk waɗanda ke son cutar da fararen hula ba tare da la’akari da addinin su ba.

A taron na Abuja, Mashawarci ga Shugaban Ƙasa kan Tsaron Ƙasa, Malam Nuhu Ribaɗu, shi ne ya jagoranci tawagar Nijeriya wadda ta ƙunshi Ma’aikatun Gwamnati da hukumomi guda 10, yayin da Ƙaramar Sakataren Harkokin Waje ta Amurka, Allison Hooker, ta jagoranci tawagar Amurka wadda ta ƙunshi hukumomin tarayyar ƙasar guda takwas.

A takardar bayan taron wadda aka raba wa manema labarai a ranar Alhamis, an bayyana cewa tattaunawar dabaru a zaman da aka yi sun mayar da hankali ne kan fannoni da dama na batutuwa da ƙalubale inda haɗin gwiwar Amurka da Nijeriya zai inganta ’yancin yin addini tare da ƙarfafa tsaro a faɗin ƙasar nan.

Ɓangarorin biyu sun yi la’akari da cewa akwai fa daɗaɗɗiyar alaƙa a tsakanin ƙasashen biyu, wadda ta ginu bisa ƙimomin haɗin kai na al’ummomi masu bambancin ra’ayi, girmama doka da oda, da mutunta ikon ƙasa.

Ɓangaren Amurka sun yi maraba da bayanin sake daidaita albarkatun Nijeriya domin magance rashin tsaro, musamman a jihohin Arewa-ta-Tsakiya. Gwamnatocin biyu sun sake jaddada ƙudiri mai ƙarfi da ba ya sassauci na kare ƙa’idojin ’yancin yin addini, tare da buƙatar ɗaukar matakai na haɗin gwiwa, masu ɗorewa da aiki tuƙuru, domin haɓakawa da kare ’yancin faɗar albarkacin baki, taron lumana, da ’yancin addini ko aƙida ga kowa, daidai da Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Nijeriya.

Mahartan taron sun kuma jaddada muhimmancin kare jama’a farar hula, musamman al’ummar Kirista masu rauni, da kuma ɗaukar matakin hukunta masu aikata tashin hankali.

Ɓangarorin biyu sun sake tabbatar da aniyar su ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwar yaƙi da ta’addanci, ciki har da aiki tare ta fannin ayyukan haɗin gwiwa na aiki, samun damar amfani da fasaha, yaƙi da safarar kuɗi ba bisa ƙa’ida ba, hana tallafa wa ta’addanci da kuɗi, da gina ƙarfin hukumomin tsaro da bincike.

Tawagar Amurka ta gode wa Nijeriya bisa matakan gaggawa da ta ɗauka na ƙarfafa tsaro ga al’ummar Kiristoci da ke cikin haɗari, da kuma ’yan Nijeriya na dukkan addinai da rayuwar su take fuskantar barazana sakamakon tashin hankali da ta’addanci.

An yanke shawarar cewa za a gudanar da taro na gaba na Guruf ɗin Aikin a Amurka, a wata ranar da ta dace da ɓangarorin biyu, wadda za a tsara ta hanyar hanyoyin diflomasiyya.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali
Next Post: Jam’iyar NNPP: Abba Kabir Yusuf Yaci Amanar Mu

Karin Labarai Masu Alaka

Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Majalisar Dattawa Ta Wanke Janar Christopher Musa A Matsayin Minista Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Fara Azumin Watan Ramadan A Najeriya Da Sassan Duniya  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe 
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne Labarai
  • An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio Labarai
  • Tawagar Shirya Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Ta Ziyarci Masarautun Jihar Labarai
  • Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja Labarai
  • Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana Labarai
  • Fiye Da Mutane Miliyan Hudu Suna Fuskantar Barazanar Yunwa A Somaliya Sauran Duniya
  • Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane Tsaro
  • Yanayin Yunwa Yana Kara Ta’azarra A Somaliya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.