Ƙasar Pakistan ta bayyana a ranar Lahadi cewa tana shirin karɓar bakuncin “tattaunawa masu ma’ana” domin kawo ƙarshen rikicin da ya shafi Iran nan da kwanaki masu zuwa, duk da cewa a baya Tehran ta zargi Amurka da shirya kai farmakin ƙasa yayin da take neman tattaunawa.
Da yake magana bayan ganawar ministocin harkokin wajen yankin, Ministan Harkokin Wajen Pakistan, Ishaq Dar, ya ce sun tattauna hanyoyin da za su iya kawo ƙarshen yaƙin cikin gaggawa da kuma na dindindin a yankin, tare da yiwuwar tattaunawa tsakanin Amurka da Iran a birnin Islamabad.
Ya ce: “Pakistan za ta ji daɗin karɓar bakunci tare da sauƙaƙa tattaunawa masu ma’ana tsakanin ɓangarorin biyu nan da kwanaki masu zuwa, domin cimma cikakkiyar sulhu mai ɗorewa kan rikicin da ke gudana.” Sai dai ba a bayyana ko Amurka da Iran sun amince za su halarci tattaunawar ba.
Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka da White House ba su bayar da amsa nan take ba kan bukatar yin tsokaci game da yiwuwar tattaunawar a Pakistan.
A baya, Kakakin Majalisar Dokokin Iran, Mohammad Baqer Qalibaf, ya zargi Amurka da aikewa da saƙonnin tattaunawa yayin da a lokaci guda take shirin tura sojoji, yana mai ƙara da cewa Tehran a shirye take ta mayar da martani idan aka tura sojojin Amurka.


