Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Prime Ministan Pakistan Yace Zai Karbi Bakoncin Tattaunawar Amurka Da Iran
Published: March 25, 2026 at 3:40 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: March 25, 2026

Prime Ministan Pakistan Shebbaz Shariff, ya fada ranar talata cewa a shirye yake ya zama mai masaukin baki a shawarwari tsakanin Amurka da Iran na kawo karshen yakin na yankin Gulf, kwana daya bayan da shugaban Amurka Donald Trump, ya dakatar da barazanar da yayi na kai hari kan cibiyoyin wutan lantarki na Iran, cewa an gudanar da shawarwari masu ma’ana.

Duk da haka, Amurka tana shirin tura dubban karin sojoji daga runduna ta 82 zuwa gabas ta tsakiya, kamar yadda mutane biyu da suke da masaniya dangane da batun suka shaidawa kamfanin dillancn labarai na Reuters. Kari kan tulin dakarun da ta aike yankin, wadda hakan yake kara janyo fargabar yakin zai dauki lokaci mai tsawo.

A rubutu da ya wallafa a shafin dandalin sada zumunta na X, PM Sharif yace, Pakistan tana maraba, kuma tana bada cikakken goyon baya kan kokari da ake yi na yin shawarwari domin kawo karshen yakin.

Ahalinda ake ciki kuma, rahotanni suka ce Iran ta tsananta matsayinta kan shawarwarin yayinda tayi ruwan makamai masu linzami kan Isra’ila, kasuwar hannayen jari a Amurka ta fadi kasa, saboda fargabar babu alamar kakkautawa a rikicin da ake yi a yankin.

A wata kuri’ar neman jin ra’ayin jama’a da kamfanin dillancin labarai na Reuters da IPSOS, suka gudanar, ya nuna farin jinin shugaban Amurka Donald Trump ya zube zuwa kashi 36 cikin dari matsaya mafi karanci tunda ya koma fadar White House, saboda karin farashin mai.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Eberechi Eze Ba Zai Buga Wasannin Da Ingila Za Tayiba Arteta
Next Post: Isra’ila Zata Mamaye Lebanon

Karin Labarai Masu Alaka

SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne Labarai
An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
Amurka Ta Cire Takunkumin Da Ta Kakabawa Shugaban Venezuela Amurka
‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya Labarai
Isra’ila Zata Karbi Mutanenta A Yankin Gaza Labarai
Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

https://www.youtube.com/watch?v=sainfSmn-EQ

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dogarawan Ruwa Na Amurka Suna Yunkurin Shiga Wani jirgin Dakon Mai Da Aka Allakan Ta Da Venezuela Labarai
  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini Afrika
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Musulmai A Kasashen Duniya Da Dama Sunfara Azumin Ramadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shirin Manuniya Yau Juma’a 12.12.2026 Shirye-Shirye
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
  • Jama’a A Yankin Gulf Sun Bukaci Dakatar Da Hare Hare Daga Washington Afrika
  • Tinubu Yafara Wasu Dabaru Domin Samun Kuri’u Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.