Amurka da Isra’ila sunyi luguden wuta kan Iran a jiya talata, da ma’aikatar tsaron Amurka da ake kira Pentagon da Farisawan suka ce shine hari mafi tsanani tun fara yakin, duk da tsammanin da kasuwannin sayar da hannayen jari na duniya suka yi cewa shugaba Donald Trump zai kawo karshen yakin bada jumawa ba.
Kara jawo kalubale ga tattalin arzikin duniya, rundunar juyin juya hali ta Iran tace zata hana jigilar mai daga yankin Gulf idan Amurka da Isra’ial basu tsaida kai mata hari ba.
Sakataren ma’aikatar Tsaron Amurka Pete Hegseth yace “yau zata kasance rana da muka fi tsananta kai hare hare a cikin Iran, jiragen yaki mafi yawa, tare da amfani da bayanan sirri mai inganci,” inji sakataren a wani taro da manema labarai.
Mazauna birnin Tehran da suka yi magana da kamfanin dilancin labarai na Reuters bisa sharadin ba za’a bayyana sunayen su ba, suka ce babu inda jiragen yakin suka bari a birnin Tehran. Tace sai ka dauka jahannama. Tace ‘yayanta har tsoron bacci suke yi.
Duk da haka, kalaman shugaba Trump ranar Litinin cewa, “kusan an kammala yakin,” masu zuba jari sunyi amannar yakin zai kare nan ba da jumawa ba, kamin kassarawar da aka yi wa jigilar makamashi ta durkusar da tattalin arzikin duniya.
Shugabannin Iran suna ci gaba da nuna turjiya ko a yau talata. “Hakika bama neman a tsagaita wuta, mun hakikance cewa tilas a kwabi bakin mai tsaukana, saboda su koyi darasi, har abada ba za su kaiwa Iran hari ba, inji a kakakin majaisar dokokin kasar, Mohammmed Baqer Qalibaf, a shafinsa na X.


