Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaban Ƙasar Koriya Ta Arewa Ya Halarci Gwajin Makami Mai Linzamin Kasar
Published: December 29, 2025 at 11:16 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Kim Jong Un na Koriya ta Arewa, ya halarci wurin gwajin wasu makamai masu linzami masu cin dogon zango da kasar ta gudanar a ranar lahadi.

Kamfanin Dillancin labarai na kasar yace shugaba Kim ya bayyana cikakkiyar gamsuwarsa, a yayin da wadannan makamai masu linzami suka tashi suka bi ta inda aka auna su, kuma suka far ma inda aka yi niyya cikin teku a yamma da yankin kasar ta Koriya.

Kim ya jaddada cewa Koriya ta Arewa zata ci gaba da maida hankali kacokan wajen ingantawa da bunkasa makaman nukiliya.

Rundunar sojojin Koriya ta Kudu ta fada ranar litinin cewa dakarunta sun gano harba makamai masu linzami da aka yi da misalin karfe 8 na safiyar ranar lahadi daga yankin Sunan a kusa da Pyongyang, babban birnin Arewa.

Kamfanin dillancin labaran Yonhap na Koriya ta Kudu yace tana yiwuwa Koriya ta Arewa ta gudanar da wasu sabbin gwaje gwajen makamai masu linzami a daidai lokacin bukukuwan sabuwar shekara.

Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine
Next Post: An Farmaki ‘Yan Bindiga Da Dama A Jihar Zamfara

Karin Labarai Masu Alaka

Masar Ta Kayyade Farashin Buradi A Kasar Afrika
Ghana Ta Haramta Hakar Ma’adinai A Gandunan Dajin Data Kebe, Labarai
Farashin Mai Ya Cigaba Da Tashi Afrika
An Watse A Tattaunawar Tsakanin Rasha Da Ukraine Batare Da Cimma Matsaya Ba Labarai
Ruwa Kamar Da Bakin Kwarya Ya Haifar Da Mutuwar Mutane A Nairobi Afrika
Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5 Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Zamu Hada Kai Mu Yaki Cutar Shan’inna (Polio) Labarai
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara Afrika
  • Na Duke Tsohon Ciniki Shirye-Shirye
  • Sarkin Gombe Ya Ziyarci Gwamna Inuwa Yahaya Afrika
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan Afrika
  • ‘Yan Sandan Birnin New York Sun Karyata Zargin Jefa Bom Ga Masu Zanga Zanga Amurka
  • Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC Siyasa
  • Hadakar Gwamnatin Najeriya Da Amurka Ne Suka Kai Hari Sokoto Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.