Ranar Talata Shugabanni a kasar Australia sunyi kira ga jama’a da su kai zuciya nesa, tare da kiran a gudanar da zanga zanga a cikin lumana, bayan da arangama ta barke a birnin Sydney, tsakanin ‘Yan sanda da masu zanga zangar nuna adawa da ziyarar da shugaban Isra’ila Isaac Herzog ya kai kasar.
‘Yan sandan kasar suka ce sun kama mutane 27 ciki harda mutum 10 kan zargin cin zarafin ‘yansanda, sakamkon tarzomar da ta barke lokacin da suka dauki matakin tarwatsa mutane da suka hallara a kusa da babban dakin taro dake birnin.
Masu zanga zanga ciki harda wata ‘yar majalisar dokokin kasar daga bangaren ‘yan hamayya, sun fada cewa ‘yansanda sun ci zarafin su.
PM kasar Anthony Albanese, yace yayi takaicin tarzomar, daga nan yayi kira ga masu zanga zanga su gudanar dashi cikin lumana.
“Yan kasar Australia suna bukatar abu biyu. Ba sa son ganin an kawo rigima anan. Suna son ganin an daina kashe mutane ko Isra’ila ce take yi ko Falasdinawa, amma basa son ganin an kawo fitina anan,” PM Albanese ya gayawa wata tashar rediyon kasar Triple M.
A cikin sanarwar da ‘Yansanda suka bayar, suka ce babu rahoton an sami jikkata mai tsanani a arangamar.


