Daga Ahmad Muhammad,Bauchi
‘Yan jarida kimanin su 14 da suka fito daga kafafen yada labarai dabam -dabam suka gamu da mummunar hatsarin mota a yayin da suke cikin tawagar hukumar raya yankin Arewa Maso Gabas (NEDC)
Shugaban kungiyar Yan Jarida Na kasa reshen jihar Bauchi da ke Arewa maso gabashin Najeriya Kwamred Umar Said ya tabbatar da aukuwar lamarin.
Umar Said wanda yake jagorantan aikin yace tare suke tafiya , direban motar Yana gudu Sai taqwace ta Tashi sama ta shiga daji kafin daga bisani tayi ta dungure dasu tana zubar da mutanen da ke ciki har Allah ya tsaida su.
Ya nuna godiya wa Allah saboda ba a rasa rai ko daya ba a ciki amma an Samu munanan raunuka da asarar kayayyakin Aiki”
Ya godewa Ministan Uba Maigari Ahmadu , da Mataimakin Gwamnan Jihar Bauchi Muhammadu Awwal Jatau, da Shugaba da Manajin Darektan Hukumar NEDC sauran Ma’aikatan Hukumar da ‘Yanjaridu saboda yadda suka nuna damuwarsu kan abinda ya faru da Kuma yadda suka tsaya Kan lamarin.
Lokacin da abin ya faru Yan jaridun suna tafiya ne a ƙarƙashin jagorancin ƙaramin ministan raya yankuna, Alhaji Uba Maigari Ahmadu a yayin da suke yawon buɗewa da miƙa ayyukan da hukumar NEDC ta gudanar a jihar Bauchi zuwa hannun gwamnatin jihar.
Hatsarin ya faru ne a kan titin Yashi zuwa Yelwan Duguri da ke cikin ƙaramar hukumar Alkaleri a jihar Bauchi da ke tarayyar Najeriya a yau ranar Jumma’a, bayan ministan ya qaddamar da katafaren makaranta a garin Yalwan Duguri.
‘yan jaridun sun samu munanan raunuka raunuka daban-daban yayin da ake ƙoƙarin samar musu da agajin gaggawa a asibitin Yelwan Duguri daga bisani kuma za a wuce da su babban asibiti a Bauchi domin neman musu kulawar likitoci.
‘Yan jaridun da abin ya Shafa waɗanda suka fito daga gidajen talabijin na Channels, AIT, NTA, BATV,Arise da wasu irin su wakilan manyan jaridun na Guardian, the nation, kamfanin dillancin labarai Na Nijeriya (News agency of Nigeria) (NAN) da sauransu da dama.
Hatsarin ya faru ne jimkaɗan bayan da tawagar suka buɗe aikin makarantar GSS a Yelwan Duguri inda suke kan hanyarsu ta zuwa domin buɗe wasu ayyukan.
Daga cikin waɗanda suke cikin tawagar har da minista, shugabannin NEDC, chairman da MD, mataimakin gwamnan jihar Bauchi da sauransu.
Kazalika, Wakilinmu wanda ke cikin tawagar ya shaida mana cewa motar da ta gamu da hatsarin ɗaya ce daga cikin motocin da ‘yan jaridan ke amfani da su a yayin aikin ɗauko labarin. Ya kuma tabbatar mana da cewa kayayyakin aikin jarida dama kamar su Kamarori sun lalace. Amma Babu asarar rai.


