Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Tinubu Ya Kawo Ƙarshen Aikin Kwamitin Sayar Da Kaddarorin Gwamnati
Published: July 30, 2026 at 8:21 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da rushe Kwamitin Shugaban Ƙasa mai kula da aiwatar da harkokin sayar da kaddarorin Gwamnatin Tarayya (Presidential Implementation Committee – PIC), tare da ba da umarnin aiwatar da matakin nan take.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar, inda ya bayyana cewa daga yanzu dukkan harkokin da suka shafi ayyukan kwamitin za su koma ƙarƙashin kulawar Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Prince Lateef Fagbemi.

Sanarwar ta tuna cewa an kafa kwamitin ne a shekarar 2000, a zamanin mulkin tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo, domin kula da sayarwa da bayar da hayar filaye da sauran kaddarorin Gwamnatin Tarayya a ƙarƙashin tsarin Monetisation Policy.

Ta ce bayan nazari mai zurfi, Gwamnatin Tarayya ta gano cewa ayyukan kwamitin sun kauce daga ainihin manufar da aka kafa shi domin aiwatarwa, lamarin da ya janyo ƙararraki masu yawa a kotuna a sassan ƙasar nan.

A sakamakon haka, gwamnatin ta yanke hukuncin cewa babu wata buƙatar ci gaba da wanzuwar kwamitin.

Saboda haka, Shugaba Tinubu ya umarci a rushe kwamitin daga ranar 5 ga Nuwamban 2025, tare da ɗora wa Babban Lauyan Tarayya alhakin kula da dukkan harkokin da suka shafi ayyukan kwamitin.

Haka kuma, Shugaban Ƙasar ya umarci tsohon Sakataren kwamitin, B. S. Dutsin-Ma, da ya dakatar da duk wani aiki ko wakilci da yake yi a madadin kwamitin ko Gwamnatin Tarayya kan duk wani lamari da ya shafi ayyukansa.

Sanarwar ta ce matakin wani ɓangare ne na ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya na inganta yadda ake tafiyar da harkokin kadarorin gwamnati cikin tsari, gaskiya da inganci.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sana'o'i, Sauran Duniya, Shirye-Shirye, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Haɗin Gwiwar GOSERC Da Savannah Zai Ƙarfafa Rarraba Wutar Lantarki A Faɗin Jihar Gombe
Next Post: Gwamnatin Najeriya Ta Jaddada Aniyarta Ta Daƙile Yaɗuwar Makamai Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Karin Labarai Masu Alaka

ECOWAS Ta Saka Dokar Ta Baci A Afrika Ta Yamma Afrika
Na Yi Murabus Ne Don Amurka Ta Keta Haddin Iraniyawa Amurka
Majami’ar Anglican Zasuyi Taron Zaben Sabon Shugaba Afrika
Kasar Faransa Zata Bunkasa Nukiliyarta Afrika
Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya Afrika
An Damke Matasa Masu Gurza Kudaden Ketare Na Jabu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23 Afrika
  • An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan Afrika
  • Ministan Sadarwan Kasar Uganda Yayi Allah Wadai Da Kaiwa Bobi Wine Hari Afrika
  • Masu Goyon Bayan Palasdinawa Sunyi Gangamin Zanga Zanga A Australia Labarai
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai
  • INEC Mayar Da Lokacin Zaɓen 2027 Kafin Azumi Najeriya
  • Samar Da Albarkatun Mai Ya Ragu A Iraq Afrika
  • Ga Fili Ga Doki Dambarwar APC Da ADC Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.