Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC
Published: December 18, 2025 at 5:47 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Tinubu ya tabbatar da naɗin shugabannin Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC)

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da sake naɗa sabon kwamitin gudanarwa na Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC), biyo bayan tabbatar da su da Majalisar Dattawa ta yi a ranar 16 ga Disamba.

A cikin sanarwar da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar, an bayyana cewa Dokta Mulisiu Olalekan Oseni ne sabon Shugaban Hukumar (Chairman), Dokta Oseni, wanda ya fara aiki a NERC a matsayin Kwamishina tun watan Janairun 2017, daga bisani ya riƙe muƙamin Mataimakin Shugaba, Naɗinsa a matsayin Shugaba ya fara aiki ne daga 1 ga Disamba, 2025, kuma zai ci gaba har zuwa cikar wa’adin sa na shekaru goma, kamar yadda Dokar Wutar Lantarki ta 2023 ta tanada.

Haka kuma, Dokta Yusuf Ali ya zama Mataimakin Shugaban Hukumar (Vice Chairman) kuma An fara naɗa shi a matsayin Kwamishina a watan Fabrairun 2022, kuma sabon muƙaminsa zai fara aiki daga 1 ga Disamba, 2025, har zuwa ƙarshen wa’adinsa na farko.

Sauran mambobin kwamitin sun haɗa da Nathan Rogers Shatti da Dafe Akpeneye, waɗanda dukkansu ke kan wa’adin su na biyu bayan an fara naɗa su a watan Janairun 2017, Haka kuma, Aisha Mahmud Kanti Bello na ci gaba da wa’adinta na biyu, bayan an fara naɗa ta a watan Disambar 2020.

A ɓangaren sababbin mambobi, Dokta Chidi Ike na kan wa’adinsa na farko tun bayan naɗinsa a watan Fabrairun 2022, yayin da Dokta Fouad Animashaun ya fara wa’adinsa na farko daga Disamba, 2025. Dokta Animashaun ƙwararren masani ne a fannin tattalin arzikin makamashi, kuma ya taɓa zama Babban Kwamishina kuma Shugaban Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Jihar Legas.

Shugaba Tinubu ya buƙaci mambobin kwamitin NERC da su ƙara ƙaimi wajen zurfafa sauye-sauyen da ake yi a ɓangaren wutar lantarki a Nijeriya, tare da bin tanade-tanaden Dokar Wutar Lantarki ta 2023 gaba ɗaya.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya
Next Post: Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000 Najeriya
Majalisa Ta Sanya Baki Akan Rikici Tsakanin Dangote Da Hukumar Albarkatun Mai Najeriya
Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki Najeriya
Matatar Man Dangote Ta Samu Tagomashi Daga Abokan Hulda Najeriya
Motar Kungiyar Kwallon Kafar Bayelsa United Ta Yi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet
  • Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Hukumar NAHCON Ta Kamallah Shirye Shiryen Hajjin 2026 A Kasar Saudiya Labarai
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC Siyasa
  • Kasar Amurka Da Rasha Zasu Kawo Karshen Tsagaita Nukiliya Amurka
  • NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas Najeriya
  • Ansamu Maganin Da Yake Rage Kitsen Jijiyoyi A Amurka Amurka
  • Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Najeriya
  • CBN: An Samu Ƙaruwar Masu Cin Bashin Banki Basa Biya Najeriya
  • Shugaban Rasha Yafara Ganawa Da Jakadun Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Ukraine Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.