Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC
Published: December 18, 2025 at 5:47 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Tinubu ya tabbatar da naɗin shugabannin Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC)

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da sake naɗa sabon kwamitin gudanarwa na Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC), biyo bayan tabbatar da su da Majalisar Dattawa ta yi a ranar 16 ga Disamba.

A cikin sanarwar da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar, an bayyana cewa Dokta Mulisiu Olalekan Oseni ne sabon Shugaban Hukumar (Chairman), Dokta Oseni, wanda ya fara aiki a NERC a matsayin Kwamishina tun watan Janairun 2017, daga bisani ya riƙe muƙamin Mataimakin Shugaba, Naɗinsa a matsayin Shugaba ya fara aiki ne daga 1 ga Disamba, 2025, kuma zai ci gaba har zuwa cikar wa’adin sa na shekaru goma, kamar yadda Dokar Wutar Lantarki ta 2023 ta tanada.

Haka kuma, Dokta Yusuf Ali ya zama Mataimakin Shugaban Hukumar (Vice Chairman) kuma An fara naɗa shi a matsayin Kwamishina a watan Fabrairun 2022, kuma sabon muƙaminsa zai fara aiki daga 1 ga Disamba, 2025, har zuwa ƙarshen wa’adinsa na farko.

Sauran mambobin kwamitin sun haɗa da Nathan Rogers Shatti da Dafe Akpeneye, waɗanda dukkansu ke kan wa’adin su na biyu bayan an fara naɗa su a watan Janairun 2017, Haka kuma, Aisha Mahmud Kanti Bello na ci gaba da wa’adinta na biyu, bayan an fara naɗa ta a watan Disambar 2020.

A ɓangaren sababbin mambobi, Dokta Chidi Ike na kan wa’adinsa na farko tun bayan naɗinsa a watan Fabrairun 2022, yayin da Dokta Fouad Animashaun ya fara wa’adinsa na farko daga Disamba, 2025. Dokta Animashaun ƙwararren masani ne a fannin tattalin arzikin makamashi, kuma ya taɓa zama Babban Kwamishina kuma Shugaban Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Jihar Legas.

Shugaba Tinubu ya buƙaci mambobin kwamitin NERC da su ƙara ƙaimi wajen zurfafa sauye-sauyen da ake yi a ɓangaren wutar lantarki a Nijeriya, tare da bin tanade-tanaden Dokar Wutar Lantarki ta 2023 gaba ɗaya.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya
Next Post: Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
Dangote Ya Bukaci ICPC Ta Binciki Shugaban NMDPRA Najeriya
Za A Rantsar Da Mainasara Kogo A Matsayin Shugaban Kundin Da’ar Ma’aikata Labarai
Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya
An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya
Mace Ta Farko Da Zata Shugabanci Jami’ar Northwest Dake Kano Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa
  • Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11
  • Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC
  • Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000 Najeriya
  • Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma Afrika
  • PDP Zata Karbi Mulki 2027 Inji Shugabannin Jam’iyar Siyasa
  • Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi Afrika
  • Ruwan Sama Ya Dai-Daita ‘Yan Gudun Hijira A Gaza Labarai
  • Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026, Labarai
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Kara Sace Mutane A Jihar Naija! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.