Shugaban Amurka Donald Trump ya yi tayin sasanta rigimar dake tsakanin kasashen Masar da Habasha game da rikicin kogin Nile da ya ratsa kasashen biyu.
Trump ya ce a shirye yake da ya shiga tsakani domin kawo karshen takaddama kan yadda rabon ruwan kogin Nile ze kasance tsakanin kasashen biyu ta hanyar da ta dace, a wata takarda da ya aikewa shugaban kasar Masar Abdel Fattah al-Sisi, wadda kuma aka wallafa a shafin sa na Truth social.
Kaddamar da wani babban madatsan ruwa da kasar fadar gwamnati a Addis Ababa ta yi ranar 9 ga Watan Satumbar bara ya jawo fushin fadar gwamnatin Cairo dake kasa daga kogin Nile.
Habasha, wadda ita ce ta biyu a mafi yawan mutane, a nahiyar Afirka, da suka kai fiye da miliyan 120, na ganin dam din da ta gina zai taka muhimmiyar rawa wajen tattalin arzikin kasar.
Masar kuma a nata bangaren ta ce dam din ya sabawa yarjejeniyar kasa da kasa, kuma zai iya jawo fari da ambaliyar ruwa duka, Habasha ta ki amincewa da hakan.
Trump ya yabawa Sisi a baya, har ya zuwa lokacin da ya je Masar a watan Oktoba domin sa hannu kan yarjejeniyar da ta Shafi rikicin Gaza.
Da ya ke tsokaci game da abin, Trump ya maimaita damuwar da fadar gwamnatin Cairo ke da shi game da maganar ruwan.


