Wasu kasashen turai suna tunani ko su daina tura jami’an su zuwa wata cibiyar soja da Amurka ta kafa domin tsara al’amura a Gaza, suna cewa cibiyar ta gaza bada damar a kara kai kayan agaji a zirin, da kuma kawo sauyi na siyasa, wasu jami’an difilomasiyya suka ce.
Cibiyar wacce gamayyar ma’aikata farar hula da sojoji, an kafa ta ne a cikin watan Oktoban bara a kudancin Isra’ila, karkashin wani shirin shugaba Trump na kawo karshen yakin Gaza. An azawa cibiyar alhakin sa ido kan yarjejeniyar tsagaita wuta da Isra’ila da Hamas suka kulla, samar da damar kara kai kayan agaji a Gaza, da kuma pullo da tsare tsare da manufofi ga yankin Falasdinawa.
Kasashe masu yawa, ciki harda Jamus, da Faransa,da Britaniya, da Masar, da hadaddiyar daular larabawa, duk sun tura jami’an su da sojoji, da masu aikin leken siri, da zummar ganin yadda al’amura za su tafi kan batun Falasdinawa.
Amma wasu manyan jami’an difilomasiyya su takwas sun gayawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, tun bayan hutun kirsimeti da na sabuwar shekara, kasashen da dama wakilan su ba su koma cibiyar ba. Saboda a cewar su babu alkibla a ayyukan cibiyar.


