Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

‘Yan Sanda A Gombe Sun Jaddada Shirin Yaƙi Da Munanan Dabi’u
Published: May 4, 2026 at 11:03 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya jaddada shirye-shiryen rundunar ‘yan sanda wajen magance munanan dabi’u a tsakanin matasa a fadin jihar.

Kwamishinan ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a taron hulɗa da al’umma da wayar da kai kan yaƙi da munanan dabi’u ta hanyar aikin ‘yan sanda wanda aka gudanar a Gombe International Hotel.

Ya ƙara da cewa yana da tsare-tsare na ƙarfafa aikin ‘yan sanda na rigakafi ta hanyar haɗin gwiwa da shugabannin addinai, shugabannin al’umma da sarakunan gargajiya, da sauran masu ruwa da tsaki.

A saƙonnin fatan alheri, Shugaban ƙungiyar Kiristoci ta CAN a jihar Gombe, Reverend Joseph Alphonsus Shenga, da Shugaban Jama’atu Nasril Islam a jihar, Alhaji Saleh Danburam, tare da Ibrahim Yusuf 3000, sun ba da tabbacin goyon bayansu ga shirye-shiryen Kwamishinan ‘yan sanda na yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi, daba, da kuma inganta tsaron al’umma ta hanyar aikin ‘yan sanda na rigakafi.

Sun kuma yaba da jajircewar Kwamishinan ‘yan sandan tare da kira ga samar da isassun jami’an tsaro a muhimman sassan jihar domin ƙarfafa ƙoƙarin yaƙi da rashin tsaro.

Da yake nasa jawabin, mai riƙe da sarautar Wazirin Yeriman Gombe, Alhaji Yaya Hammari, ya yi bayani kan tarihin aikin ‘yan sanda a jihar, inda ya yaba da ƙirƙirar wannan taro na hulɗa da al’umma wanda zai taimaka wajen rage munanan dabi’u.

Ya bayyana cewa shan kayan maye a tsakanin matasa na haddasa rashin aikin yi da sauran matsaloli a cikin al’umma, tare da kira ga bayar da cikakken goyon baya da haɗin kai domin samun nasara.

Shi ma Shugaban PCRC na jihar Gombe, Kwamared Garba Ubale, ya ce wannan shiri na Kwamishinan abin a yaba ne, yana mai cewa wannan shi ne karo na uku da aka gudanar a ƙarƙashin jagorancin CP Ahmed Chuso.

Ya kuma yaba da ƙoƙarin DPO na Pantami bisa fahimta da jajircewa, tare da kira da a ƙara ƙaimi wajen yaƙi da munanan dabi’u domin ci gaban al’umma.

A nasa ɓangaren, Abdulaziz Sani Labaran na Youth O’Clock, a cikin takardar da ya gabatar, ya bayyana cewa wasu ‘yan siyasa da wasu na taimakawa wajen jefa matasa cikin shan kayan maye, inda ya buƙaci a ɗauki matakan da za su kawo ƙarshen lamarin.

A takardar daya Gabatar Malami Daga Sashin ilimin halayyar Dan Adam na jami’ar jihar Gombe Dr. Ahmad Adamu ya bayyana aikin tsaro a matsayin Wani muhimmin aiki Wanda yake taimakawa Wajen kyautata rayuwar al’umma.

Dr. Ahmad Yace akwai kwarewa tare da salo ayyukan Jami’an Tsaro Wajen Kawo Karshen matsalar Tsaro a cikin al’umma, inda ya bukaci Samun hadinkan al’umma wajen Samun nasarar Abunda aka Saka a gaba.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sanata Goje Yayi Watsi Da Fidda ‘Yan Takarar APC A Gombe
Next Post: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Katsina

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Amurka,Israela Da Iran Sun Amince Da Dakatar Da Yaki Afrika
Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
Dan Gudun Hijira Tarique Rahman Ya Kusa Zama Shugaban Kasa Labarai
Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
Kotu A Najeriya Ta Kame Mutane Bisa Zargin Ta’addaci Afrika
Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Tsinto Gawarwakin ‘Yan gudun Hijira A Bakin Tekun Comoros Labarai
  • NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
  • Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro Labarai
  • Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela Amurka
  • Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro Tsaro
  • Kotu A Najeriya Ta Kame Mutane Bisa Zargin Ta’addaci Afrika
  • Hawan Sallah A Jihar Katsina Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.