‘Yan sanda a Habasha ko Ethiopia sunce sun kama dubban albarusai da Eritrea ta aikawa ‘yan tawaye a yankin Amhara, zargin da Eritean tayi watsi da shi a zaman kariya da Ethiopia ta zuka da nufin kafa hujjar ta afka yaki.
Zargin da rundunar ‘Yansandan kasar Ethiopia tayi ya zafafa rikici tsakanin kasashen biyu, da suka jima suna gaba da juna, amma suka kulla yarjejeniyar zaman lafiya a 2018, wadda tuni sabbin barazana tsakanin kasashen biyu yake maye gurbinta.
A cikin sanarwar data bayar a daren ranar Laraba, rundunar ‘Yan sandan a habashan tace ta kama albarusai dubu 56,000, ta kama mutane biyu a yankin Amhara cikin makon nan, yankin da kungiyar ‘yan tawaye da ake kira Fano take kaddamar da hare hare da turjiya tun a shekarar 2023.
Ministan yada labarai a Eritrea Yemane Gebremeskel, ya fadawa kamfain dillancin labarai na Reuters cewa, jam’iyyar PP ta PM Abiy Ahmed, tana neman wata hujjar da zata fake dashi domin ta kai farmaki.
Tunda a farkon wannan mako a hira da yayi a kafofin yada labaran Erirea, shugaban kasar Isaias Afwerki, yace jam’iyyar PP a Habasha ta ayyana yaki kan kasarsa.
Kasashen biyu sun gwabza yaki kan rikicin kan iyaka rikici da ya barke a shekara ta 1998, shekaru biyar bayan da Eritrea ta sami ‘yancin kai daga kasar Habasha ko Ethiopia.


