Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji A Kauyen Wanka Jihar Filato
Published: March 16, 2026 at 8:27 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Al’ummar kauyen Wanka dake karamar hukumar Kanam a Jihar Filato sun nemi hukumomi su kai musu dauki, bayan watsewarsu daga kauyen, biyo bayan kisan sojoji da ‘yan banga da ‘yan ta’adda suka yi a karshen makon jiya.

Garin Wanka, wanda ke yankin Garga a karamar hukumar Kanam a jihar Filato, na makwabtaka da karamar hukumar Alkalerin jihar Bauchi kusa da dajin da ‘yan bindiga ke cin karensu babu babbaka.

Wani mazaunin garin na Wanka da ya bukaci in sakaya sunanshi saboda tsaro, yace ‘yan bindigar sun kashe sojoji goma sha hudu da ‘yan banga biyar, lamari kenan da ya sanya suka watse daga kauyen.

Duk da cewa kafafen yada labarai sun yayata batun kisan sojojin, rundunar dake wanzadda zaman lafiya a yankin, Operation Enduring Peace bata fitar da sanarwa kan batun ba.

Bayanai sun nuna cewa sojojin da aka kashen suna aikin tabbatar da tsaro ne a yankin, kafin ‘yan bindigar su yi musu kwanton bauna suka hallaka su.

Haka ma bayanan da ba’a tantance ba sun nuna cewa sojoji sun hallaka ‘yan ta’adda fiye da ishirin a yankin na Wanka.

A wata sanarwa da gwamnatin jihar Filato ta fitar da sanya hannun komishinan yada labarai da sadarwa, Madam Joyce Ramnap tace gwamnati na kan bakanta na tsaron lafiyar jama’a da dukiyoyinsu.

Sanarwar tace gwamnati ta hada gwiwa da jami’an tsaro don kara azama wajen tabbatar da tsaro a dukkan yankunan dake fuskantar barazanar tsaro a fadin jihar.

Mai fashin baķi kan lamura kuma sakataren kungiyar dake raya al’ummar Kanam, Nuhu Shehu Kanam yace matsalar tsaro a yankin ba sabon abu bane amma hukumomi sun kasa shawo kanta.

Bayanai na nuni da cewa ayyukan masu bada bayanai wa ‘yan ta’adda, da aka fi sani da informants, suna tasiri wajen samun cikkas da yaki da matsalolin tsaro a yankin na Garga da kewaye.

Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/AUD-20260316-WA0040.mp3
Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sarkin Musulmi Ya Ziyarci Shugaba Bola Tinubu
Next Post: Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
An Zargi Babban Mai Gabatar Da Kara A Kotun Duniya Ta ICC Afrika
Sojojin Kasar Isra’ila Sun Kashe Wani Babban Kwamandan Hamas Labarai
Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar Afrika
Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci Afrika
An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Fubara Yana Yiwa Dimokraɗiyya Zagon Kasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa Labarai
  • Gwamna Abba Gida-Gida Na Dari-Darin Shiga APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kotu A Kasar Tunisiya Ta Daure Wani Babban Dan Kasuwa Da Wasu ‘Yan Majalisa Afrika
  • Shugaba Bola Tinubu Ya Tafi Turai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage Afrika
  • Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana Amurka
  • Sojojin Kasar Isra’ila Sun Kashe Wani Babban Kwamandan Hamas Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.