Al’ummar kauyen Wanka dake karamar hukumar Kanam a Jihar Filato sun nemi hukumomi su kai musu dauki, bayan watsewarsu daga kauyen, biyo bayan kisan sojoji da ‘yan banga da ‘yan ta’adda suka yi a karshen makon jiya.
Garin Wanka, wanda ke yankin Garga a karamar hukumar Kanam a jihar Filato, na makwabtaka da karamar hukumar Alkalerin jihar Bauchi kusa da dajin da ‘yan bindiga ke cin karensu babu babbaka.
Wani mazaunin garin na Wanka da ya bukaci in sakaya sunanshi saboda tsaro, yace ‘yan bindigar sun kashe sojoji goma sha hudu da ‘yan banga biyar, lamari kenan da ya sanya suka watse daga kauyen.
Duk da cewa kafafen yada labarai sun yayata batun kisan sojojin, rundunar dake wanzadda zaman lafiya a yankin, Operation Enduring Peace bata fitar da sanarwa kan batun ba.
Bayanai sun nuna cewa sojojin da aka kashen suna aikin tabbatar da tsaro ne a yankin, kafin ‘yan bindigar su yi musu kwanton bauna suka hallaka su.
Haka ma bayanan da ba’a tantance ba sun nuna cewa sojoji sun hallaka ‘yan ta’adda fiye da ishirin a yankin na Wanka.
A wata sanarwa da gwamnatin jihar Filato ta fitar da sanya hannun komishinan yada labarai da sadarwa, Madam Joyce Ramnap tace gwamnati na kan bakanta na tsaron lafiyar jama’a da dukiyoyinsu.
Sanarwar tace gwamnati ta hada gwiwa da jami’an tsaro don kara azama wajen tabbatar da tsaro a dukkan yankunan dake fuskantar barazanar tsaro a fadin jihar.
Mai fashin baķi kan lamura kuma sakataren kungiyar dake raya al’ummar Kanam, Nuhu Shehu Kanam yace matsalar tsaro a yankin ba sabon abu bane amma hukumomi sun kasa shawo kanta.
Bayanai na nuni da cewa ayyukan masu bada bayanai wa ‘yan ta’adda, da aka fi sani da informants, suna tasiri wajen samun cikkas da yaki da matsalolin tsaro a yankin na Garga da kewaye.
Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton Daga Jos


