Kawowa yanzu dai yawan wadanda suka mutu a mummunan harin yanbindiga a Jihar kwaran Najeriya yakai 170 a ciki harda wasu Jami,an tsaron yanbanga sama da goma da aka kona su kurmus,
Acikin daren jiya talata ne dai maharan dauke da manyan da ake zaton Yan Kungiyar jihadi ne na ISWAP suka auka garin woro dake karamar hukumar kayama ta Jihar kwara lamarin da ya jefa daturuwan mazauna garin cikin tashin hankali,
Hon.Abubakar Abdullahi Danladi shine Shugaban karamar Hukumar ta kayama yace suna cikin yanayi na tashin hankali Amma Kuma sun Maida al’amarin ga Allah..
Dan Majalisar Dokokin Jihar kwara Mai wakiltar karamar Hukumar kayama Hon.Sa,idu baba Ahmed yace duk da yake mutane 78 sukayi Jana,Izar bai daya a lokaci guda Amma wadanda aka kashe sun Kai 170 sannan da Wasu yanbindiga goma sha Uku da aka kona kurmus da Kuma Wasu yayan Sarkin garin guda biyu da aka kashe,Dan Majalisar yace maharan sun wuce da wasu mata 30 a ciki harda Matan sarkin guda biyu.ā

Ayanzu alummomin Yankin Borgu a Jihar Neja da Kuma Yankin kayama ta jihar kwara na cike da fatar ganin Gwamnatin Najeriya ta daukin yin wani cikin hanzari akan Gandun dajin nan na Kainji domin kawar da maharan da suka maida gandun dajin Mafakarsu.

