Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya
Published: November 25, 2025 at 8:38 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 25, 2025

Hukumar abinci ta Majalisar Dinkin Duniya (MDD) ta ce hare-haren ‘yan bindiga a yankin Arewacin Najeriya zai haddasa bala’in rashin abinci da ya fi na ko’ina muni a Nahiyar Afirka a cikin shekara mai zuwa.

A wani rahoton da hukumar ta wallafa yau Talata, ta yi kiyasin cewa mutane kimanin miliyan 35 zasu iya fuskantar yunwa a Najeriya a shekara mai zuwa, wanda zai kasance shine mafi muni a duk fadin nahiyar Afirka, kuma mafi muni da za a gani a cikin Najeriya tun daga lokacin da hukumar ta fara tattara irin wadannan alkaluma.

Hukumar ta kuma ce akwai mutane kimanin dubu 15 da zasu fuskanci bala’in mummunar yunwa mai iya kaiwa ga hallaka a Jihar Borno a shekara mai zuwa. Hukumar zata dora jihar Borno a mataki na 5 na bala’in yunwa, wanda shine matakin mafi muni na rashin abinci, kamar irin yadda ake gani a Gaza da Sudan.

Hukumar, wadda ake kira WFP a takaice, ta ce yankin Arewacin Najeeriya zai fuskanci bala’in yunwa mafi muni da bai taba gani ba cikin shekaru 10, inda manoma da mazauna karkara zasu fi shan wahala.

Jami’ain suka ce hare-haren ‘yan bindiga dabam dabam sun hana manoma yin amfani da gonakinsu a Arewa, yayin da a watan Oktoba aka samu wata sabuwar kungiyar ‘yan ta’addar da ita ma ta shiga cikin Najeriya. Wannan kungiya mai suna Jama’at Nusrat al-Islam wal Muslimin, ta saba kai hare-hare a yankin bakin iyakar Nijar, Mali da Burkina Faso.

Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi
Next Post: Gangamin Wayar Da Kai Don Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Jihar Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya
Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
An Samu Nasarar Karbo Karin Yara 130 Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
NAHCON Tafara Shirye-Shiryen Aikin Hajjin 2026 Najeriya
Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
Baba Buhari Yayi Zargin Ansaka Masa Na’urar Tsaro Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Soke Bashin Da Gwamnati Take Bin NNPC Najeriya
  • Jirgin Ruwa Ya Kife A Yammacin Kasar Gambiya Labarai
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Gyara Dokar Kasafin Kudi Labarai
  • Kyautata Dangantaka Tsakanin Jami’an Tsaro Da Al’umma Ce Mafita Najeriya
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Kocin Ranchers Bees Ya Yi Murabus Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.