Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

‘Yan Sanda Sun Kama Masu Garkuwar da Mutane a Jihar Gombe
Published: December 6, 2025 at 8:35 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe ta bayyana cewa ta kama mutum bakwai da ake zargi da hannu a ayyukan masu garkuwa da mutane da kuma satar shanu a fadin jihar.

A cewar sanarwar da rundunar ta fitar dauke da sahannun Jami’in hulda da jama’a na rundunar DSP Buhari Abdullah, an kama Abdullahi Ibrahim mai shekaru 40 a garin Tilde dake karamar hukumar Funakaye, a ranar 23 ga Nuwamba, 2025, bayan samun sahihan bayanai daga wani mai kishin kasa da suka zargeshi da boye masu laifi.

A yayin bincike, Abdullahi ya amsa laifin sa, inda ya bayyana cewa yana da hannu a satar shanu da kuma wasu hare haren masu garkuwa da mutane a fadin jihar Gombe.

Haka kuma ya fadi sunayen wasu abokan aikin sa da suka hada kai wajen gudanar da miyagun ayyukan a jihohin Gombe, Bauchi, Yobe da jihar Adamawa.

Rundunar ta ce a bisa wannan bayani ne jami’an ‘yan sanda da ke Operation Hattara tare da hadin gwiwar kungiyar masunta na jihar Gombe suka kai samame a wasu maboyar miyagun, inda aka yi musayar wuta da suka kai ga cafke karin mutum shida.

Wadanda aka kama sun hada da, Usman Mohammed, mai shekaru 30,Hussain Idris, mai shekaru 37, Adamu Tukur, mai shekaru 37 ,Yau Abdullahi, mai shekaru 25 da Ali Umar, mai shekaru 18 sai Hassan Usman, mai shekaru 40 da kuma Abdullahi Ibrahim, mai shekaru 40, daga Tilde,Karamar Hukumar Funakaye jihar Gombe

Sannan Rundunar ta tabbatar da ci gaba da gudanar da bincike tare da shirin gurfanar da su a gaban kotu.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026.
Next Post: Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA.

Karin Labarai Masu Alaka

Ankara Gano Wani Abu Mai Kama Da Abun Fashewa A Jabo Jihar Sokoto Tsaro
An Gudanar Da Addu’oi Ga Mutane 16 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Australiya Tsaro
An Gurfaranar Da Wadanda Ake Zargi Takai Hari Gaban Kotu Najeriya
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar Labarai
Kasar China Ta Kaddamar Da Rawar Daji A Yankin Taiwan Labarai
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC Siyasa
  • Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa Labarai
  • Adamu: “Yakar Cin Hanci Daga Tushe Itace Mafita Daya Tilo” Labarai
  • Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi Labarai
  • Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika
  • Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu Najeriya
  • Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro Tsaro
  • Kasar Canada Ta Amince A Shigar Da Motoci Kirar Kasar China Kasar Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.