Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery
Published: December 7, 2025 at 4:13 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 7, 2025

‘Yan bindiga sun hallaka Malaman makaranta a gundumar Filingue da ke yankin Tilabery iyakar Nijar da Mali.
Lamarin ya tada hankulan uwar kungiyar malaman makaranta wace ta yi kiran hukumomi su tsaurara matakai a yankunan da ke fama da matsalolin tsaro donganin an ci gaba da karantarwa a makarantun boko.
Lamarin ya faru ne a ranar Juma’a lokacin da wadanan malamai da suka hada da darektan makarantar kauyen Sabon garin Takoussa Abdoulaye Askou da takwaransa na makarantar kauyen Maitalakia Nouhou Oumarou na kan hanyar zuwa taron kwamitin COGES da aka gudanar a Filingue lokacin da maharan suka afka masu kamar yadda kungiyar malaman kwantaragi ta SYNACEB ta bayyana a sanarwar nuna juyayi da ta fitar.
Wannan ba shi ne karon farko da ‘yan bindiga ke far wa malaman makaranta ba kokuma dakunan karantun da kansu a yankunan da ke fama da matsalolin tsaro sabili kenan SYNACEB ke tunar da mahakunta a kan bukatar karfafa matakai domin dorewar sha’anin ilimi.
Kawo yanzu ba wata sanarwa daga bangaren gwamnati a kan wannan al’amari. Na tuntubi mai bai wa ministar ilimi shawara Issoufou Arzika ta waya to amma ya mayar da ni wajen jami’ar hulda da ‘yan jarida Hadiza Issa wace ba ta daga wayarta ba lokacin da na kira ta sannan ba ta amsa sakon text din da na tura ma ta har zuwa lokacin aika wannan rahoto.
Yankin Tilabery mai iyaka da Burkina Faso da Mali na daga cikin yankuna mafi fama da barazanar ‘yan bindiga lamarin da tun a wajejen 2017 ya haddasa rufe makarantu da dama koda ya ke a Watan satumban da ya gabata ministar ilimi Dr Elizabeth Cherif ta sanar cewa yawan irin wadanan makarantu ya ragu.
To amma ya mayar da ni wajen jami’ar hulda da ‘yan jarida Hadiza wace ba ta daga wayarta ba lokacin da na kirata sannan ba ta amsa sakon text din da na tura ma ta har zuwa lokacin aika wannan rahoto.
KISAN MALAMAN MAKARANTA
Afrika

Post navigation

Previous Post: ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji
Next Post: Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade

Karin Labarai Masu Alaka

Dan Hamayya Ya Amince Da Faduwa A Zaben Kasar Benin Afrika
‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano Afrika
Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika
Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
Boko Haram Ta Kai Hari Maiduguri Cikin Dare Afrika
Shugaba Tinubu Ya Shiga Takara Wa’adi Na Biyu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu Sauran Duniya
  • Najib Razak Zai Kara Shekaru 15 A Gidan Yari Saboda Cin Zarafin Kujerar Mulki Labarai
  • Okoye Na Shirin Maye Gurbin Nwabali, AFCON 2025: Wasanni
  • Shugaban Kasar Iran Yace Kasar Bata Da Kiyayya Tsakaninta Da Amurkawa Afrika
  • Sojojin Amurka Sun Kutsa Cikin Kasar Iran Labarai
  • Ferfesa Pantami Yayi Watsi Da Amincewa Da Jamilu Isiyaku Gwamna Afrika
  • Gwamnatin Kasar Benin Ta Nemi ‘Yan Kasa Su Kwantar Da Hankali Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.