Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika

‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery
Published: December 7, 2025 at 4:13 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 7, 2025

‘Yan bindiga sun hallaka Malaman makaranta a gundumar Filingue da ke yankin Tilabery iyakar Nijar da Mali.
Lamarin ya tada hankulan uwar kungiyar malaman makaranta wace ta yi kiran hukumomi su tsaurara matakai a yankunan da ke fama da matsalolin tsaro donganin an ci gaba da karantarwa a makarantun boko.
Lamarin ya faru ne a ranar Juma’a lokacin da wadanan malamai da suka hada da darektan makarantar kauyen Sabon garin Takoussa Abdoulaye Askou da takwaransa na makarantar kauyen Maitalakia Nouhou Oumarou na kan hanyar zuwa taron kwamitin COGES da aka gudanar a Filingue lokacin da maharan suka afka masu kamar yadda kungiyar malaman kwantaragi ta SYNACEB ta bayyana a sanarwar nuna juyayi da ta fitar.
Wannan ba shi ne karon farko da ‘yan bindiga ke far wa malaman makaranta ba kokuma dakunan karantun da kansu a yankunan da ke fama da matsalolin tsaro sabili kenan SYNACEB ke tunar da mahakunta a kan bukatar karfafa matakai domin dorewar sha’anin ilimi.
Kawo yanzu ba wata sanarwa daga bangaren gwamnati a kan wannan al’amari. Na tuntubi mai bai wa ministar ilimi shawara Issoufou Arzika ta waya to amma ya mayar da ni wajen jami’ar hulda da ‘yan jarida Hadiza Issa wace ba ta daga wayarta ba lokacin da na kira ta sannan ba ta amsa sakon text din da na tura ma ta har zuwa lokacin aika wannan rahoto.
Yankin Tilabery mai iyaka da Burkina Faso da Mali na daga cikin yankuna mafi fama da barazanar ‘yan bindiga lamarin da tun a wajejen 2017 ya haddasa rufe makarantu da dama koda ya ke a Watan satumban da ya gabata ministar ilimi Dr Elizabeth Cherif ta sanar cewa yawan irin wadanan makarantu ya ragu.
To amma ya mayar da ni wajen jami’ar hulda da ‘yan jarida Hadiza wace ba ta daga wayarta ba lokacin da na kirata sannan ba ta amsa sakon text din da na tura ma ta har zuwa lokacin aika wannan rahoto.
KISAN MALAMAN MAKARANTA
Afrika

Post navigation

Previous Post: ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji
Next Post: Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade

Karin Labarai Masu Alaka

Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia Afrika
An Gano Kwale-Kwalen Fir’auna A Birnin Masar Afrika
Jama’a A Yankin Gulf Sun Bukaci Dakatar Da Hare Hare Daga Washington Afrika
Gwamnatin Najeriya Tana Saka Ido Akan Matsalolin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yaki Da Akeyi Tsakanin Isra’ila Da Amurka Afrika
Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist
    Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo Wasanni
  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba Afrika
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari A Lebanon Afrika
  • ‘Yan Bindiga A Mali Sun Kashe Direbobin Manyan Motoci Afrika
  • An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
  • Gwamnatin Shugaba Trump Tana Cigaba Da Janye Jakadunta Zuwa Gida Amurka
  • Kamfanin Bitcoin A Korea Ta Kudu Yayi Kuskuren Turawa Masu Mu’amala Da Kamfanin Kudade Afrika
  • Iran Zata Kawo Karshen Yaki Da Isra’ila Da Amurka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.